< Proverbi 1 >

1 Proverbi di Salomone, figlio di Davide, re d'Israele,
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 per conoscere la sapienza e la disciplina, per capire i detti profondi,
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 per acquistare un'istruzione illuminata, equità, giustizia e rettitudine,
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 per dare agli inesperti l'accortezza, ai giovani conoscenza e riflessione.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Ascolti il saggio e aumenterà il sapere, e l'uomo accorto acquisterà il dono del consiglio,
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 per comprendere proverbi e allegorie, le massime dei saggi e i loro enigmi.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 Il timore del Signore è il principio della scienza; gli stolti disprezzano la sapienza e l'istruzione.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Ascolta, figlio mio, l'istruzione di tuo padre e non disprezzare l'insegnamento di tua madre,
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 perché saranno una corona graziosa sul tuo capo e monili per il tuo collo.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Figlio mio, se i peccatori ti vogliono traviare, non acconsentire!
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 Se ti dicono: «Vieni con noi, complottiamo per spargere sangue, insidiamo impunemente l'innocente,
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 inghiottiamoli vivi come gli inferi, interi, come coloro che scendon nella fossa; (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 troveremo ogni specie di beni preziosi, riempiremo di bottino le nostre case;
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 tu getterai la sorte insieme con noi, una sola borsa avremo in comune»,
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 figlio mio, non andare per la loro strada, tieni lontano il piede dai loro sentieri!
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 I loro passi infatti corrono verso il male e si affrettano a spargere il sangue.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Invano si tende la rete sotto gli occhi degli uccelli.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 Ma costoro complottano contro il proprio sangue, pongono agguati contro se stessi.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Tale è la fine di chi si dà alla rapina; la cupidigia toglie di mezzo colui che ne è dominato.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 La Sapienza grida per le strade nelle piazze fa udire la voce;
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 dall'alto delle mura essa chiama, pronunzia i suoi detti alle porte della città:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 «Fino a quando, o inesperti, amerete l'inesperienza e i beffardi si compiaceranno delle loro beffe e gli sciocchi avranno in odio la scienza?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Volgetevi alle mie esortazioni: ecco, io effonderò il mio spirito su di voi e vi manifesterò le mie parole.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Poiché vi ho chiamato e avete rifiutato, ho steso la mano e nessuno ci ha fatto attenzione;
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 avete trascurato ogni mio consiglio e la mia esortazione non avete accolto;
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 anch'io riderò delle vostre sventure, mi farò beffe quando su di voi verrà la paura,
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 quando come una tempesta vi piomberà addosso il terrore, quando la disgrazia vi raggiungerà come un uragano, quando vi colpirà l'angoscia e la tribolazione.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Allora mi invocheranno, ma io non risponderò, mi cercheranno, ma non mi troveranno.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Poiché hanno odiato la sapienza e non hanno amato il timore del Signore;
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 non hanno accettato il mio consiglio e hanno disprezzato tutte le mie esortazioni;
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 mangeranno il frutto della loro condotta e si sazieranno dei risultati delle loro decisioni.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Sì, lo sbandamento degli inesperti li ucciderà e la spensieratezza degli sciocchi li farà perire;
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 ma chi ascolta me vivrà tranquillo e sicuro dal timore del male».
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Proverbi 1 >