< Zefanya 3 >

1 Terkutuklah Yerusalem, kota bejat yang suka memberontak terhadap TUHAN dan yang menindas penduduknya sendiri!
Taki ta ƙare, ke birnin mai danniya, mai’yan tawaye da kuma masu ƙazanta!
2 Celakalah kota yang tidak mau menerima peringatan TUHAN, dan tidak pula mengindahkan teguran-teguran-Nya, yang tidak menyerahkan nasibnya kepada TUHAN, dan tidak meminta tolong kepada-Nya!
Ba kya yi wa kowa biyayya, ba kya kuma yarda da kuskurenki. Ba kya dogara ga Ubangiji, ba kya kuma kusatowa kusa da Allahnki.
3 Pembesar-pembesar kota itu seperti singa yang mengaum-aum. Hakim-hakimnya seperti serigala-serigala lapar; mereka sangat serakah sehingga satu tulang pun tak ada yang ditinggalkan untuk besoknya.
Sarakunanki ruri ne na zakoki, shugabanninki kyarketan dare ne, waɗanda ba sa rage kome don safe.
4 Nabi-nabinya tidak punya rasa tanggung jawab dan tidak dapat dipercaya; para imam menajiskan apa yang dikhususkan untuk TUHAN dan memutarbalikkan hukum-hukum Allah untuk keuntungan mereka sendiri.
Annabawanki mahaukata ne mutanenki masu cin amana ne. Firistocinki suna ƙazantar da Wurin Mai Tsarki suna kuma keta dokoki.
5 Tetapi TUHAN masih ada di kota itu; Ia selalu melakukan yang benar dan tidak pernah yang salah. Setiap pagi pastilah Ia memberi keadilan kepada umat-Nya. Namun, orang yang tidak kenal keadilan di kota itu tetap berbuat jahat tanpa kenal malu.
Ubangiji da yake cikinki mai adalci ne; ba ya yin abin da ba daidai ba. Kowace safiya yakan bayyana dokokinsa a fili, kowace sabuwar rana kuma ba ya kāsawa, duk da haka marasa adalci ba sa jin kunya.
6 TUHAN berkata, "Aku telah melenyapkan banyak bangsa; kota-kota mereka Kuhancurkan, dan tembok-tembok serta menara-menara mereka Kujadikan puing-puing. Kota-kota mereka sunyi tanpa penghuni dan jalan-jalannya lengang.
“Na daddatse al’ummai; an kuma rurrushe kagararsu. Na bar titunansu ba kowa, ba mai ratsawa a ciki. An ragargaza biranensu; ba wanda za a bari, babu ko ɗaya.
7 Pikir-Ku, 'Sekarang pastilah umat-Ku menghormati Aku dan mengindahkan segala teguran-Ku. Tentulah mereka mengingat pelajaran yang Kuberikan kepada mereka.' Tetapi nyatanya, mereka lebih giat lagi berbuat jahat daripada sebelumnya.
Na ce wa birnin, ‘Tabbatacce za ki ji tsorona ki kuma yarda da gyara!’ Ta haka ba za a datse wurin zamanki ba, ba kuwa dukan hukuncena za su hau bisa kansu ba. Amma har yanzu suna marmari su yi rashin gaskiya a duk abin da suke yi.
8 Tetapi awas! Tunggu saja harinya Aku bangkit sebagai pengadu. Sebab sudah Kuputuskan untuk mengumpulkan bangsa-bangsa dan kerajaan-kerajaan guna menimpakan murka-Ku ke atas mereka. Seluruh bumi akan habis dimakan api kemarahan-Ku.
Saboda haka ku jira ni,” in ji Ubangiji; “a ranar da zan tsaya in ba da shaida, Na yanke shawara in tattara dukan al’ummai, in tattara mulkoki in kuma zuba fushina a kansu, da dukan zafin haushina. Za a mamaye dukan duniya da zafin fushina.
9 Tetapi kemudian Aku akan mengubah hati bangsa-bangsa itu, sehingga mereka berdoa kepada-Ku saja, dan tidak kepada ilah-ilah lain. Bangsa-bangsa itu semua akan mentaati Aku.
“Sa’an nan zan tsarkake leɓunan mutanen, don dukansu su kira bisa ga sunan Ubangiji su kuma yi masa hidima kafaɗa da kafaɗa.
10 Bahkan dari Sudan yang jauh, umat-Ku yang tercerai-berai itu akan datang dan mempersembahkan kurban kepada-Ku.
Tun daga ƙetaren rafuffukan Kush masu yi mini sujada, mutanena da suke a warwatse, za su kawo mini hadayu.
11 Pada waktu itu, hai umat-Ku, kamu tak perlu merasa malu lagi karena telah memberontak terhadap Aku. Aku akan mengusir setiap orang yang sombong dan angkuh, dan kamu tidak akan memberontak lagi terhadap Aku di bukit-Ku yang suci.
A wannan rana ba za ku sha kunya saboda laifofin da kuka yi mini, gama zan ɗauke wa wannan birni waɗanda suke farin ciki cikin girmankansu. Ba kuma za ka ƙara yin kallon reni a tuduna mai tsarki ba.
12 Di sana akan Kubiarkan menetap suatu bangsa yang rendah hati, yang mengandalkan pertolongan-Ku. Mereka boleh tinggal di sana.
Amma zan zauna a cikinki masu tawali’u da masu ƙasƙantar da kai, waɗanda suke dogara ga sunan Ubangiji.
13 Orang Israel yang masih tersisa, tidak akan berbuat jahat lagi kepada siapa pun; mereka tak akan berbohong lagi dan tidak pula menipu. Mereka akan makmur dan sejahtera, dan tidak merasa takut kepada siapa pun."
Raguwar Isra’ila ba za su ƙara aikata abin da ba daidai ba, ba za su faɗa ƙarya ba, ba kuwa za a sami ruɗu a bakunansu ba. Za su ci su kuma kwanta kuma babu wanda zai ba su tsoro.”
14 Hai Israel, bersoraklah dan bernyanyi! Hai Yerusalem, bergembiralah dengan segenap hati!
Ki rera, ya Diyar Sihiyona; ki tā da murya, ya Isra’ila! Ki yi murna ki kuma yi farin ciki da dukan zuciyarki, Ya Diyar Urushalima!
15 Sebab TUHAN berhenti menghukum kamu; Ia telah mengusir segala musuhmu. Kamu dilindungi oleh raja Israel, Tuhanmu sendiri. Sekarang kamu tak perlu merasa takut lagi.
Ubangiji ya ɗauke hukuncinki, ya mai da abokan gābanki baya. Ubangiji, Sarkin Isra’ila, yana tare da ke; ba kuma za ki ƙara jin tsoron wani lahani ba.
16 Akan tiba saatnya orang-orang akan berkata nanti, "Hai Yerusalem, janganlah takut dan tawar hati.
A wannan rana za su cewa Urushalima, “Kada ki ji tsoro, ya Sihiyona; kada ki bar hannuwanki su raunana.
17 Kamu dilindungi oleh TUHAN Allahmu yang perkasa. Kamu menang karena kuasa-Nya. TUHAN gembira dan bersukacita karena kamu, dalam kasih-Nya diberi-Nya kamu hidup baru.
Ubangiji Allahnki yana tare da ke, mai iko ne don ceto. Zai yi matuƙar farin ciki da ke, zai rufe ki da ƙaunarsa, zai yi farin ciki da ke ta wurin rerawa.”
18 Karena kamu, Ia bernyanyi gembira seperti orang yang sedang berpesta." Kata TUHAN, "Malapetaka yang mengancam kamu Kutiadakan. Kehinaanmu telah Kuhapuskan.
“Zan cire taƙaici daga gare ki a ƙayyadaddun bukukkuwa; su kaya ne da kuma zargi a gare ki.
19 Masanya akan datang penindasmu Kuhancurkan, dan orang pincang Kuselamatkan; semua buangan Kubimbing pulang. Kehinaan mereka Kuubah menjadi kehormatan; di mana saja, bahkan di seluruh bumi, mereka akan dimuliakan dan dipuji.
A wannan lokaci zan jijji wa waɗanda suka danne ku; zan kuɓutar da guragu in kuma tattara waɗanda suke a warwatse. Zan sa a yabe su a kuma girmama su a kowace ƙasar da aka kunyatar da su.
20 Masanya akan datang, pendudukmu yang terpencar Kubimbing pulang. Kamu Kubuat tenar di seluruh muka bumi, dan kemakmuranmu akan Kupulihkan lagi." TUHAN telah berbicara.
A wannan lokaci zan tattara ku; a wannan lokaci zan kawo ku gida, zan sa a yabe ku a kuma girmama ku a cikin dukan mutanen duniya a sa’ad da na maido da arzikinku a idanunku,” in ji Ubangiji.

< Zefanya 3 >