< Mazmur 89 >

1 Nyanyian pengajaran Etan, orang Ezrahi.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Sebab aku tahu kasih-Mu kekal abadi, kesetiaan-Mu teguh seperti langit.
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 Engkau berkata, "Aku sudah membuat perjanjian dengan orang pilihan-Ku; Aku telah bersumpah kepada Daud, hamba-Ku:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 'Takhtamu Kupertahankan untuk selama-lamanya, turun-temurun anak cucumu akan mendudukinya.'"
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Sidang surgawi memuji perbuatan-perbuatan-Mu yang ajaib, dan menyanyikan kesetiaan-Mu, TUHAN.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Di langit tak ada yang seperti Engkau, ya TUHAN, tak ada makhluk surgawi yang menyamai Engkau.
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Engkau dihormati di kalangan para suci, ditakuti lebih dari semua di sekeliling-Mu.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 TUHAN, Allah Yang Mahakuasa, siapakah sekuat Engkau? Engkau setia dalam segala-galanya ya TUHAN.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Engkau menguasai laut yang bergelora, dan meredakan ombaknya yang dahsyat.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Rahab, naga laut, Kauremukkan dan Kaubunuh, dengan tangan kuat Kaukalahkan musuh-musuh-Mu.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Langit dan bumi adalah milik-Mu, dunia dan segala isinya ciptaan-Mu.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Engkaulah yang menjadikan utara dan selatan, Gunung Tabor dan Hermon bersorak-sorai bagi-Mu.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Betapa besar kuasa-Mu, dan betapa hebat kekuatan-Mu!
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Keadilan dan hukum adalah dasar kerajaan-Mu, kasih dan kesetiaan nyata dalam segala tindakan-Mu.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Berbahagialah bangsa yang beribadat dengan gembira, yang hidup dalam cahaya kehadiran-Mu, TUHAN.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 Sepanjang hari mereka bersukacita dan tetap teguh, karena kebaikan-Mu.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Engkau memberi kami kemenangan yang gilang-gemilang, karena kebaikan-Mulah kami menang.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Sebab pelindung kami adalah orang pilihan-Mu, ya TUHAN; raja kami adalah milik Allah Kudus Israel.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Dahulu kala dalam suatu penglihatan, Engkau berkata kepada hamba-Mu yang setia, "Aku telah menolong seorang pahlawan, seorang yang Kupilih dari rakyat telah Kutinggikan.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 Aku telah menemukan Daud, hamba-Ku, dan Kulantik dia dengan minyak upacara.
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Kekuatan-Ku akan selalu melindunginya, kuasa-Ku akan menguatkan dia.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 Ia tak akan dikalahkan musuh, dan tak akan ditindas orang jahat.
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 Semua musuhnya akan Kubinasakan, Kubunuh siapa saja yang membenci dia.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 Aku akan tetap mengasihi dia dan setia kepadanya, dan membuat dia semakin berkuasa.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Kerajaannya akan Kuluaskan, dari Laut Tengah sampai ke Sungai Efrat.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Ia akan berkata kepada-Ku, 'Engkaulah Bapaku, Allahku, pelindung dan penyelamatku.'
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Aku akan menjadikan dia putra-Ku yang sulung, yang paling agung di antara semua raja.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Dia akan tetap Kukasihi sampai kekal, perjanjian-Ku dengan dia tetap teguh.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Takhtanya Kupertahankan selama langit ada di atas bumi, turun-temurun anak cucunya akan mendudukinya.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Tetapi kalau keturunannya melanggar hukum-Ku, dan tidak hidup menurut perintah-Ku,
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 kalau mereka tidak mengindahkan ketetapan-Ku dan mengabaikan peraturan-Ku,
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 mereka Kuhukum dengan cambuk karena pelanggarannya, dan Kutimpa dengan bencana karena dosa-dosanya.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Tetapi Aku akan tetap mengasihi Daud, dan tak akan mengingkari kesetiaan-Ku.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Perjanjian-Ku dengan dia takkan Kubatalkan, dari janji-Ku tak satu pun Kutarik kembali.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Sekali untuk selamanya Aku bersumpah demi nama-Ku yang suci; Aku tak akan berbohong kepada Daud.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Takhtanya akan bertahan selama matahari ada, turun-temurun anak cucunya akan mendudukinya.
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Kerajaannya tetap ada seperti bulan, saksi setia di awan-awan."
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Tetapi sekarang Engkau marah kepada raja, Engkau membuang dan menolak orang pilihan-Mu.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Kaubatalkan perjanjian-Mu dengan hamba-Mu, mahkotanya Kaulemparkan ke dalam lumpur.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Kaurobohkan tembok-tembok kotanya, benteng-benteng Kaujadikan reruntuhan.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Semua orang yang lewat merampas miliknya, ia menjadi bahan ejekan bagi tetangganya.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Engkau memberi kemenangan kepada musuh-musuhnya, dan membuat semua lawannya bergembira.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Bahkan senjatanya Kaujadikan tak berguna, Engkau tidak menolong dia dalam perang.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Kauakhiri kuasanya yang semarak, takhtanya Kaucampakkan ke tanah.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Engkau memperpendek masa mudanya, dan menutupi dia dengan malu.
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Sampai kapan Engkau bersembunyi, ya TUHAN? Sampai kapan kemarahan-Mu berkobar seperti api?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Ingatlah aku betapa singkatnya hidupku ini, Kauciptakan manusia sebagai makhluk yang fana.
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Siapakah yang dapat hidup terus dan tidak mati? Siapakah yang dapat luput dari kuburan? (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Ya TUHAN, di manakah tanda kasih-Mu yang semula, yang Kaujanjikan kepada Daud demi kesetiaan-Mu?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Ingatlah ya TUHAN, bagaimana hamba-Mu ini dicela, aku menanggung penghinaan banyak bangsa.
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 Musuh-musuh-Mu menghina raja pilihan-Mu, ya TUHAN, mengejek dia ke mana saja ia pergi.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Pujilah TUHAN untuk selama-lamanya. Jadilah demikian! Amin!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Mazmur 89 >