< Mazmur 46 >

1 Mazmur kaum Korah. Untuk pemimpin kor. Dengan lagu Alamot. Allah adalah perlindungan dan kekuatan kita; Ia selalu siap dan mampu menolong dalam kesesakan.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
2 Maka kita tidak takut, biarpun bumi bergoncang, dan gunung-gunung tenggelam ke dasar lautan;
Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
3 biar laut mengamuk dan bergelora, dan bukit-bukit gemetar oleh pukulannya.
ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
4 Ada aliran sungai yang menggembirakan kota Allah, tempat kediaman Allah Yang Mahatinggi.
Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
5 Allah berdiam di sana, maka kota itu takkan musnah; Ia akan menolongnya waktu fajar merekah.
Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
6 Allah mengguntur, maka bumi hancur luluh; bangsa-bangsa gempar, kerajaan-kerajaan runtuh.
Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
7 TUHAN Yang Mahakuasa menyertai kita, Allah Yakub melindungi kita.
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
8 Mari, lihatlah apa yang dikerjakan TUHAN; betapa menakjubkan karya-Nya di bumi!
Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
9 Ia menghentikan peperangan di seluruh dunia, busur dan lembing dihancurkan-Nya, perisai-perisai bundar dibakar-Nya.
Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
10 Kata-Nya, "Berhentilah berperang; ketahuilah, Aku ini Allah, Aku agung di antara bangsa-bangsa, agung di seluruh bumi."
“Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
11 TUHAN Yang Mahakuasa menyertai kita, Allah Yakub melindungi kita.
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)

< Mazmur 46 >