< Mazmur 25 >

1 Mazmur Daud. Kepada-Mu, ya TUHAN, kupanjatkan doaku,
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 ya Allahku, aku percaya kepada-Mu! Jangan biarkan aku dipermalukan, dan disoraki musuh-musuhku.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Orang yang berkhianat kepada-Mu akan dipermalukan, tetapi yang percaya kepada-Mu tak akan dikecewakan.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Tunjukkanlah kehendak-Mu kepadaku, ya TUHAN, nyatakanlah apa yang harus kulakukan.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Ajarilah dan bimbinglah aku untuk hidup menurut kehendak-Mu, sebab Engkaulah Allah yang menyelamatkan aku, aku selalu berharap kepada-Mu.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Ingatlah kebaikan dan kasih-Mu, ya TUHAN, yang Kautunjukkan sejak semula.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Ampunilah dosa dan kesalahan masa mudaku, ingatlah aku sesuai dengan kasih dan kebaikan-Mu.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 Sebab TUHAN baik dan adil, Ia menunjukkan jalan kepada orang yang sesat.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 TUHAN membimbing orang yang rendah hati, dan mengajar mereka kehendak-Nya.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 Orang yang taat pada perjanjian dan hukum-Nya, diperlakukan-Nya dengan kasih dan setia.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 TUHAN, ampunilah aku sesuai dengan janji-Mu, sebab besarlah kesalahanku.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 TUHAN mengajarkan kepada orang takwa jalan yang harus mereka tempuh.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 Mereka akan tetap hidup makmur, anak cucu mereka akan mewarisi tanah pusaka.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 TUHAN adalah sahabat orang yang takwa, Ia menyatakan maksud-Nya kepada mereka.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Mataku tetap terarah kepada TUHAN, sebab Ia menyelamatkan aku dari bahaya.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Pandanglah aku, dan kasihani aku, sebab aku kesepian dan sengsara.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 Kesusahan hatiku semakin bertambah bebaskanlah aku dari kesesakanku.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Perhatikanlah sengsara dan kesukaranku, dan ampunilah semua dosaku.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Lihatlah betapa banyak musuhku; mereka sangat membenci aku.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Jagalah dan selamatkanlah aku, supaya aku tidak mendapat malu, sebab aku berlindung pada-Mu.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Semoga kebaikan dan kejujuran mengawal aku, sebab aku berharap kepada-Mu.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Ya Allah, bebaskanlah umat-Mu dari segala kesesakannya.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Mazmur 25 >