< Mazmur 140 >

1 Untuk pemimpin kor. Mazmur Daud. Lepaskanlah aku dari orang jahat, ya TUHAN, jagalah aku terhadap orang yang melakukan kekerasan.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
2 Mereka merencanakan kejahatan dalam hati, dan setiap hari menimbulkan pertengkaran.
masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
3 Lidah mereka seperti ular berbisa, kata-kata mereka seperti racun ular sendok.
Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
4 Ya TUHAN, lindungilah aku dari kuasa orang jahat, jagalah aku terhadap orang yang melakukan kekerasan yang bermaksud untuk menjatuhkan aku.
Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
5 Orang congkak diam-diam memasang jerat bagiku, dan membentangkan jaring untuk menangkap aku. Di sepanjang jalan mereka memasang perangkap untuk menjebak aku.
Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
6 Ya TUHAN, aku berkata: Engkaulah Allahku, perhatikanlah doa permohonanku.
Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
7 TUHAN, Allahku, penyelamatku yang kuat, Engkau telah melindungi aku dalam pertempuran.
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
8 Jangan kabulkan keinginan orang jahat, ya TUHAN, jangan biarkan rencana mereka berhasil.
Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
9 Jangan biarkan musuhku menang; biarlah kata-kata jahat yang mereka ucapkan menimpa diri mereka yang memfitnah aku.
Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
10 Biarlah mereka dihujani bara api, dan dibuang ke dalam lubang maut, sehingga tak bisa keluar lagi.
Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
11 Biarlah orang yang melakukan kekerasan ditimpa malapetaka, jangan biarkan pemfitnah mendiami bumi.
Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
12 Aku tahu Engkau memberi keadilan kepada orang tertindas, dan membela perkara orang miskin.
Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
13 Orang jujur akan memuji Engkau; mereka akan tinggal bersama-Mu.
Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.

< Mazmur 140 >