< Amsal 23 >

1 Jika engkau duduk makan dengan seorang pembesar, ingatlah siapa dia.
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 Bila engkau mempunyai nafsu makan yang besar, tahanlah keinginanmu itu.
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Jangan rakus akan makanan enak yang dihidangkannya, barangkali ia hendak menjebak engkau.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Janganlah bersusah payah untuk menjadi kaya. Batalkanlah niatmu itu.
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 Sebab, dalam sekejap saja hartamu bisa lenyap, seolah-olah ia bersayap dan terbang ke angkasa seperti burung rajawali.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Jangan makan bersama orang kikir. Jangan pula ingin akan makanannya yang lezat.
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 Sebab, ia akan berkata, "Mari makan; silakan tambah lagi," padahal maksudnya bukan begitu. Ia bermulut manis, tapi hati lain.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 Nanti apa yang sudah kautelan kaumuntahkan kembali, dan semua kata-katamu yang manis kepadanya tak ada gunanya.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 Janganlah menasihati orang bodoh; ia tidak akan menghargai nasihatmu itu.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Jangan sekali-kali memindahkan batas tanah warisan atau mengambil tanah kepunyaan yatim piatu.
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 Sebab, TUHAN adalah pembela yang kuat dialah yang akan membela mereka melawan engkau.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Perhatikanlah ajaran gurumu dan belajarlah sebanyak mungkin.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Janganlah segan-segan mendidik anakmu. Jika engkau memukul dia dengan rotan, ia tak akan mati,
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 malah akan selamat. (Sheol h7585)
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
15 Anakku, aku senang sekali kalau engkau bijaksana.
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 Aku bangga bila mendengar engkau mengucapkan kata-kata yang tepat.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Janganlah iri hati kepada orang berdosa. Taatlah selalu kepada Allah
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 supaya masa depanmu terjamin, dan harapanmu tidak hilang.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Dengarkan, anakku! Jadilah bijaksana. Perhatikanlah sungguh-sungguh cara hidupmu.
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Janganlah bergaul dengan pemabuk atau orang rakus,
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 sebab mereka akan menjadi miskin. Jika engkau tidur saja, maka tak lama lagi engkau akan berpakaian compang-camping.
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Taatilah ayahmu; sebab, tanpa dia engkau tidak ada. Apabila ibumu sudah tua, tunjukkanlah bahwa engkau menghargai dia.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Ajaran yang benar, hikmat, didikan, dan pengertian--semuanya itu patut dibeli, tetapi terlalu berharga untuk dijual.
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 Seorang ayah akan gembira kalau anaknya mempunyai budi pekerti yang baik; ia akan bangga kalau anaknya bijaksana.
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 Semoga ayah ibumu bangga terhadapmu; semoga bahagialah wanita yang melahirkan engkau.
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 Perhatikanlah baik-baik dan contohilah hidupku, anakku!
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 Perempuan nakal yang melacur adalah perangkap yang berbahaya.
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 Mereka menghadang seperti perampok dan membuat banyak laki-laki berzinah.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Tahukah engkau apa yang terjadi pada orang yang minum anggur terlalu banyak, dan sering mengecap minuman keras? Orang itu sengsara dan menderita. Ia selalu bertengkar dan mengeluh. Matanya merah dan badannya luka-luka, padahal semuanya itu dapat dihindarinya.
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 Janganlah membiarkan anggur menggodamu, sekalipun warnanya sangat menarik dan nampaknya berkilauan dalam gelas serta mengalir masuk dengan nikmat ke dalam tenggorokan.
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 Esok paginya engkau merasa seperti telah dipagut ular berbisa.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Matamu berkunang-kunang, pikiranmu kacau dan mulutmu mengoceh.
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 Engkau merasa seperti berada pada ujung tiang kapal di tengah lautan; kepalamu pusing dan engkau terhuyung-huyung.
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 Lalu kau akan berkata, "Rupanya aku dipukul dan ditampar orang, tetapi aku tak dapat mengingat apa yang telah terjadi. Aduh, aku ngantuk sekali! Aku perlu minum lagi!"
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”

< Amsal 23 >