< Amsal 2 >

1 Terimalah ajaran-ajaranku, anakku, dan ingatlah selalu akan nasihat-nasihatku kepadamu.
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 Perhatikanlah apa yang bijaksana dan berusahalah memahaminya.
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 Ya, anakku, berusahalah untuk mempunyai pikiran yang tajam dan mintalah pengertian.
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 Carilah itu seperti mencari emas, dan kejarlah itu seperti mengejar harta yang terpendam.
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Dengan demikian kau akan tahu apa artinya takut akan TUHAN dan kau akan mendapat pengetahuan tentang Allah.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Tuhanlah yang memberikan hikmat; dari Dialah manusia mendapat pengetahuan dan pengertian.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 Kepada orang yang tulus dan tak bercela, diberikan-Nya pertolongan dan perlindungan.
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 TUHAN menjaga orang-orang yang berlaku adil, dan melindungi mereka yang mencintai Dia.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Kalau engkau menuruti aku, anakku, engkau akan tahu apa yang adil, jujur dan baik. Kau akan tahu juga bagaimana caranya kau harus hidup.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Kau akan menjadi bijaksana, dan pengetahuanmu akan menyenangkan hatimu.
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Pengertian dan kecerdasanmu akan melindungimu,
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 serta mencegah engkau mengikuti cara hidup yang tidak baik, dan juga menjauhkan dirimu dari orang-orang yang bermulut jahat.
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 Mereka tak mau mengikuti cara hidup yang baik; mereka mengambil jalan yang gelap dan penuh dosa.
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Mereka mendapatkan kesenangan dari perbuatan mereka yang jahat.
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Mereka curang dan cara hidup mereka serong.
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 Engkau, anakku, akan bisa menolak bujukan perempuan nakal yang berusaha memikat engkau dengan kata-kata yang manis.
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 Wanita itu tidak setia kepada suaminya dan telah melupakan janjinya kepada Allah.
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 Kalau engkau ke rumahnya berarti engkau menuju kematian. Pergi ke sana sama saja dengan pergi ke dunia orang mati.
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Orang yang pergi kepadanya tidak pernah ada yang kembali ke jalan yang menuju kehidupan.
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Karena itu, anakku, ikutilah teladan orang baik, dan hiduplah menurut kemauan Allah.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Sebab, orang yang hidup menurut kemauan Allah, yaitu orang yang tulus hatinya, merekalah yang akan tinggal di negeri yang dijanjikan oleh TUHAN.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 Tetapi orang jahat dan berdosa akan dilempar keluar oleh Allah dari negeri itu, seperti rumput dicabut dari tanah.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Amsal 2 >