< Bilangan 15 >

1 TUHAN memberi kepada Musa
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 peraturan-peraturan ini yang harus dilakukan oleh bangsa Israel di negeri yang akan diberikan TUHAN kepada mereka.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
3 Untuk kurban bakaran atau kurban pembayar kaul atau kurban sukarela atau kurban pada perayaan-perayaan biasa, kamu boleh mempersembahkan kepada TUHAN: sapi jantan, domba jantan, domba atau kambing. Bau kurban-kurban itu menyenangkan hati TUHAN.
kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
4 Barangsiapa mempersembahkan domba atau kambing untuk kurban bakaran kepada TUHAN, harus membawa juga bersama dengan setiap ekor ternak itu, satu kilogram tepung dicampur dengan satu liter minyak zaitun untuk kurban sajian, dan juga satu liter air anggur.
sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
5
Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
6 Kalau yang dikurbankan itu seekor domba jantan, harus dipersembahkan juga dua kilogram tepung dicampur dengan satu setengah liter minyak zaitun untuk kurban sajian,
“‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
7 dan satu setengah liter air anggur. Bau kurban itu menyenangkan hati TUHAN.
da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
8 Kalau yang dikurbankan itu seekor sapi jantan untuk kurban bakaran atau kurban pembayar kaul atau kurban perdamaian,
“‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
9 harus dipersembahkan juga tiga kilogram tepung dicampur dengan dua liter minyak zaitun untuk kurban sajian,
sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
10 dan dua liter air anggur. Bau kurban itu menyenangkan hati TUHAN.
A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
11 Itulah yang harus dipersembahkan bersama-sama dengan setiap ekor sapi jantan, domba jantan, domba atau kambing.
Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
12 Kalau yang dikurbankan itu lebih dari seekor ternak, maka persembahan tepung, minyak dan air anggur itu pun harus ditambah menurut perbandingan.
Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
13 Hal itu harus dilakukan oleh setiap orang Israel waktu ia mempersembahkan kurban. Bau kurban itu menyenangkan hati TUHAN.
“‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 Seorang asing yang tinggal di antara kamu, baik untuk sementara waktu atau untuk menetap, harus mentaati semua peraturan itu bila ia mempersembahkan kurban makanan yang baunya menyenangkan hati TUHAN.
Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
15 Semua hukum dan peraturan adalah sama untuk kamu dan untuk orang asing yang tinggal di antara kamu, sebab kamu dan mereka adalah sama dalam pandangan TUHAN. Dan hal itu berlaku untuk selama-lamanya.
Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
17 TUHAN memberi kepada Musa
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 peraturan-peraturan ini yang harus dilakukan oleh bangsa Israel di negeri yang akan diberikan TUHAN kepada mereka.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
19 Apabila kamu sudah mulai makan apa yang dihasilkan negeri itu, kamu harus menyisihkan sebagian untuk persembahan khusus bagi TUHAN.
kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
20 Kalau kamu membakar roti dari gandum yang pertama dipotong, roti itu harus dipersembahkan sebagai kurban khusus kepada TUHAN. Cara mempersembahkannya sama dengan cara mempersembahkan gandum pertama yang kamu giling.
Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
21 Untuk selama-lamanya setiap roti dari gandum yang pertama dipotong itu harus kamu berikan sebagai persembahan khusus kepada TUHAN.
A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
22 Apabila kamu dengan tidak sengaja melalaikan salah satu di antara peraturan yang telah diberikan TUHAN kepada Musa, mulai dari hari TUHAN memberi peraturan itu dan selanjutnya turun-temurun, dan kesalahan itu dibuat karena umat tidak mengetahui peraturan, maka seluruh umat harus mempersembahkan seekor sapi jantan untuk kurban bakaran. Bersama-sama dengan itu harus dipersembahkan kurban sajian dan air anggur seperti yang ditentukan. Bau kurban itu menyenangkan hati TUHAN. Selain itu harus dikurbankan seekor domba jantan untuk kurban pengampunan dosa.
“‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
25 Lalu imam harus melakukan upacara pengampunan dosa untuk umat. Maka mereka akan diampuni karena kesalahan itu mereka buat dengan tidak sengaja, dan karena mereka sudah membawa kurban pengampunan dosa serta kurban bakaran kepada TUHAN.
Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
26 Seluruh umat Israel dan orang asing yang tinggal di antara mereka akan diampuni, karena semuanya terlibat dalam kesalahan yang tidak disengaja itu.
Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
27 Apabila satu orang saja berdosa dengan tidak sengaja, maka ia harus mengurbankan seekor kambing betina yang berumur satu tahun untuk kurban pengampunan dosa.
“‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
28 Imam harus melakukan upacara pengampunan dosa di hadapan TUHAN, supaya orang itu diampuni dosanya.
Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
29 Peraturan itu berlaku juga untuk siapa saja yang berbuat dosa dengan tidak sengaja, baik dia itu orang Israel atau orang asing yang menetap di antara mereka.
Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
30 Tetapi kalau seorang Israel atau seorang asing dengan sengaja berbuat dosa, dia meremehkan TUHAN. Orang itu harus dihukum mati,
“‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
31 karena ia melawan TUHAN dan dengan sengaja melanggar perintah TUHAN. Orang itu mati karena salahnya sendiri.
gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
32 Pada waktu orang Israel berada di padang gurun, seorang laki-laki kedapatan sedang mengumpulkan kayu api pada hari Sabat.
Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
33 Orang itu dibawa menghadap Musa, Harun dan seluruh umat,
Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
34 lalu ditahan karena belum jelas ia harus diapakan.
sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
35 TUHAN berkata kepada Musa, "Orang itu harus dihukum mati. Ia harus dibawa ke luar perkemahan dan di sana seluruh umat harus melempari dia dengan batu sampai mati."
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
36 Maka seluruh umat menggiring dia ke luar perkemahan dan melempari dia dengan batu sampai mati, seperti yang diperintahkan TUHAN.
Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
37 TUHAN menyuruh Musa
Ubangiji ya ce wa Musa,
38 mengatakan kepada bangsa Israel, "Buatlah rumbai-rumbai pada ujung-ujung pakaianmu dan ikatkan tali biru pada setiap rumbai. Itu harus kamu lakukan turun-temurun.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
39 Rumbai-rumbai adalah untuk peringatan: Setiap kali kamu melihatnya, kamu ingat akan segala perintah-Ku dan mentaatinya. Dan karena itu kamu tidak akan melupakan Aku untuk mengikuti keinginan dan hasratmu sendiri.
Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
40 Rumbai-rumbai itu akan mengingatkan kamu untuk mentaati semua perintah-Ku, sehingga kamu benar-benar menjadi milik-Ku.
Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
41 Akulah TUHAN Allahmu; Aku membawa kamu keluar dari Mesir supaya Aku menjadi Allahmu, Akulah TUHAN."
Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< Bilangan 15 >