< Ayub 36 >

1 Dengarkanlah sebentar lagi, dan bersabarlah, masih ada yang hendak kukatakan demi Allah.
Elihu ya ci gaba,
2
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Pengetahuanku luas; akan kugunakan itu untuk membuktikan bahwa adillah Penciptaku.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 Perkataanku tidak ada yang palsu; orang yang sungguh arif ada di depanmu.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Allah itu perkasa! Segala sesuatu difahami-Nya. Tak seorang pun dipandang-Nya hina.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 Orang yang berdosa tak dibiarkan-Nya hidup lama, Ia memberi keadilan kepada orang yang menderita.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 Orang-orang jujur diperhatikan-Nya, dibuat-Nya mereka berkuasa seperti raja-raja, sehingga mereka dihormati selama-lamanya.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 Tetapi bila orang dibelenggu dengan rantai besi, menderita akibat perbuatannya sendiri,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 maka dosa dan kesombongan mereka akan disingkapkan oleh Allah.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 Disuruhnya mereka mendengarkan peringatan-Nya dan meninggalkan kejahatan mereka.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 Jika mereka menurut kepada Allah dan berbakti kepada-Nya, mereka hidup damai dan makmur sampai akhir hayatnya.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 Tetapi jika mereka tidak mendengarkan, mereka akan mati dalam kebodohan.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 Orang yang tak bertuhan menyimpan kemarahan; biar dihukum TUHAN, tak mau mereka minta bantuan.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Mereka mati kepayahan di masa mudanya, karena hidupnya penuh hina.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 Allah mengajar manusia melalui derita, Ia memakai kesusahan untuk menyadarkannya.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Allah telah membebaskan engkau dari kesukaran, sehingga kau dapat menikmati ketentraman, dan meja hidanganmu penuh makanan.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Tetapi kini sesuai dengan kejahatanmu, engkau menerima hukumanmu.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Waspadalah, jangan kau tertipu oleh uang sogokan; jangan kau disesatkan karena kekayaan.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Sia-sia saja kau berseru minta dibantu, percuma segala tenaga dan kekuatanmu.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Jangan kaurindukan malam gelap, saatnya bangsa-bangsa musnah dan lenyap.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Waspadalah, jangan berpaling kepada kedurhakaan. Deritamu dimaksudkan agar kautinggalkan kejahatan.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Ingatlah, Allah itu sungguh besar kuasa-Nya. Adakah guru sehebat Dia?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Siapakah dapat menentukan jalan bagi-Nya atau berani menuduh-Nya berbuat salah?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Selalu Ia dipuji karena karya-Nya, dan engkau pun patut menjunjung-Nya.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Semua orang melihat perbuatan-Nya; tetapi tak seorang pun benar-benar memahami-Nya.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Allah sungguh mulia, tak dapat kita menyelami-Nya ataupun menghitung jumlah tahun-Nya.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Allah yang menarik air dari bumi menjadi awan lalu mengubahnya menjadi tetesan air hujan.
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Ia mencurahkan hujan dari mega; disiramkan-Nya ke atas umat manusia.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Tak seorang pun mengerti gerak awan-awan serta bunyi guruh di langit tempat Allah berdiam.
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Ia menerangi seluruh langit dengan kilat, tetapi dasar laut tetap gelap pekat.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 Itulah caranya Ia menghidupi bangsa-bangsa dan memberinya makanan yang berlimpah ruah.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 Ia menangkap kilat dengan tangan-Nya dan menyuruhnya menyambar sasaran-Nya.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 Bunyi guruh menandakan bahwa badai akan melanda, ternak pun tahu angin ribut segera tiba.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Ayub 36 >