< Yesaya 34 >

1 Marilah berkumpul, hai bangsa-bangsa, dan dengarlah. Biarlah seluruh bumi dan semua yang hidup di dalamnya datang dan mendengarkan.
Ku zo kusa, ku al’ummai, ku kuwa saurara ku kasa kunne, ku mutane! Bari duniya ta ji, da kuma dukan abin da yake cikinta, duniya, da dukan abin da yake fitowa daga gare ta!
2 TUHAN marah kepada semua bangsa dan segala pasukan mereka. Ia akan menghukum dan membinasakan mereka.
Ubangiji yana fushi da dukan al’ummai; hasalarsa tana a kan mayaƙansu. Zai hallaka su tas, zai ba da su a karkashe.
3 Mayat-mayat mereka tak akan dikuburkan, tetapi dibiarkan saja menjadi busuk dan berbau. Gunung-gunung akan merah karena kebanjiran darah mereka.
Za a jefar da waɗanda aka kashe gawawwakinsu za su yi wari; duwatsu za su jiƙu da jininsu.
4 Matahari, bulan dan bintang-bintang akan hancur. Langit akan digulung seperti gulungan kertas. Bintang-bintang akan jatuh seperti daun-daun yang berguguran dari pohon.
Za a tumɓuke dukan taurarin sammai za a kuma nannaɗe sararin sama kamar littafi; dukan rundunar sama za su fāffāɗi kamar ganyayen da suka yanƙwane daga kuringa, kamar’ya’yan ɓauren da suka bushe daga itacen ɓaure.
5 TUHAN sudah menyiapkan pedang-Nya di surga, dan sekarang pedang itu akan menimpa bangsa Edom yang telah dijatuhi hukuman dan akan dibinasakan.
Takobina ya sha zararsa a cikin sammai; duba, ya sauko cikin hukunci a kan Edom, mutanen da zan hallaka tas.
6 Pedang TUHAN akan berlumuran darah dan penuh dengan lemak mereka, seperti dengan darah dan lemak binatang kurban. Sebab TUHAN menyediakan kurban di Bozra, dan mengadakan pembantaian besar-besaran di tanah Edom.
Takobin Ubangiji ya jiƙu da jini, ya rufu da kitse, jinin raguna da na awaki, kitse daga ƙodar raguna. Gama Ubangiji ya yi hadayar Bozra da kuma babban kisa a Edom.
7 Orang-orang akan tewas seperti lembu liar dan sapi muda. Negeri mereka akan merah dengan darah dan penuh dengan lemak.
Babban bijimin jeji zai fāɗi tare da su, maruƙan bijimi da manyan bijimai. Ƙasarsu za tă cika da jini, ƙura kuma zai cika da kitse.
8 Itulah saatnya TUHAN membela Sion dan membalas dendam kepada musuh-musuh-Nya.
Gama Ubangiji yana da ranar ɗaukar fansa, shekarar ramuwa, don biya wa Sihiyona bukata.
9 Sungai-sungai Edom akan berubah menjadi ter, dan tanahnya menjadi belerang. Akhirnya seluruh negeri menyala seperti ter.
Za a mai da rafuffukan Edom rami, ƙurarta za tă zama kibiritun farar wuta; ƙasarta za tă zama rami mai ƙuna!
10 Siang malam nyala itu tidak padam, dan asap mengepul daripadanya untuk selama-lamanya. Tanah itu akan ditinggalkan kosong dan gersang turun-temurun, dan tak seorang pun akan melaluinya.
Ba za a kashe ta ba dare da rana; hayaƙinta za tă yi ta tashi har abada. Daga tsara zuwa tsara za tă zama kango; babu wani da zai ƙara wucewa ta wurin.
11 Burung undan dan landak akan mendiaminya, burung hantu dan gagak akan tinggal di sana. TUHAN menjadikan tanah itu kacau dan kosong seperti sebelum penciptaan.
Mujiyar hamada da mujiya mai kuka za su mallake ta; babban mujiya da hankaka za su yi sheƙa a can. Allah zai miƙe a kan Edom magwajin bala’i da ma’aunin kango.
12 Tak ada raja yang memerintah negeri itu, dan semua pemimpinnya sudah lenyap.
Sarakunanta ba za su kasance da wani abin da ake kira masarauta ba, dukan sarakunanta za su ɓace.
13 Puri-purinya dan kota-kotanya yang berkubu akan ditumbuhi semak berduri dan rumput, dan dihuni oleh anjing hutan dan burung unta.
Ƙayayuwa za su mamaye fadodinta ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za su cika kagaranta. Za tă zama mazaunin diloli da gida don mujiyoyi.
14 Binatang buas akan berkeliaran di dalamnya; hantu-hantu bersahut-sahutan, dan hantu malam mencari tempat beristirahat.
Halittun hamada za su sadu da kuraye, awakin jeji za su yi ta kiran juna; a can halittun dare su ma za su huta su kuma nemi wurin hutu wa kansu.
15 Di tempat itu ular berbisa membuat sarangnya, bertelur, mengeram dan memelihara anak-anaknya. Burung alap-alap pun berkumpul dengan pasangannya masing-masing.
Mujiya za tă yi sheƙa a can ta zuba ƙwai; za tă ƙyanƙyashe su, ta kuma kula da’ya’yanta a inuwar fikafikanta; a can kuma shirwa za su taru, kowa da abokinsa.
16 Carilah dan bacalah dalam Kitab TUHAN: Tidak satu pun dari semua makhluk itu akan hilang atau tanpa pasangan. Sebab begitulah perintah TUHAN, dan Ia sendiri yang telah mengumpulkan mereka.
Duba a cikin littafin Ubangiji ka kuma karanta. Babu wani a cikin waɗannan da ya ɓace, babu ko ɗaya da ba ta da abokiya. Gama bakinsa ne ya ba da umarni, Ruhunsa kuma zai tara su wuri ɗaya.
17 Tuhanlah yang membagi negeri itu di antara mereka dan masing-masing menerima bagiannya. Mereka akan tinggal di situ untuk selama-lamanya, dan tanah itu menjadi milik mereka turun-temurun.
Ya ba su rabonsu; hannunsa ya rarraba musu ta wurin awo. Za su mallake ta har abada su kuma zauna a can daga tsara zuwa tsara.

< Yesaya 34 >