< Yehezkiel 29 >

1 Pada tanggal dua belas bulan sepuluh, dalam tahun kesepuluh masa pembuangan kami, TUHAN berkata kepadaku,
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Hai manusia fana, kecamlah raja Mesir. Katakanlah kepadanya bahwa dia dan seluruh rakyat Mesir akan dihukum."
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 TUHAN Yang Mahatinggi menyuruh aku menyampaikan kepada raja Mesir pesan ini, "Aku ini musuhmu, hai buaya raksasa yang berbaring di tengah sungai. Engkau membual bahwa Sungai Nil adalah milikmu dan bahwa engkaulah yang membuatnya.
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 Aku akan memasang kaitan pada rahangmu dan melekatkan ikan-ikan pada sisikmu. Lalu engkau Kutarik keluar dari Sungai Nil dengan segala ikan yang melekat pada sisikmu itu.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 Kemudian engkau dan segala ikan itu Kulemparkan ke padang pasir. Tubuhmu akan terhempas ke tanah dan terkapar di situ. Tak seorang pun akan mengubur engkau. Tubuhmu akan Kuberikan kepada burung-burung dan binatang-binatang lain untuk dimakan.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 Maka tahulah seluruh rakyat Mesir bahwa Akulah TUHAN." TUHAN berkata, "Hai bangsa Mesir! Orang Israel mengharapkan bantuanmu, tetapi ternyata engkau hanya seperti tongkat yang lemah saja.
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 Ketika mereka bersandar padamu, engkau patah dan menusuk ketiak mereka, sehingga punggung mereka terkilir.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 Oleh sebab itu Aku, TUHAN Yang Mahatinggi, mengatakan kepadamu, bahwa Aku akan mengirim tentara yang akan menyerang engkau dengan pedang, dan membunuh penduduk serta ternakmu.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 Mesir akan menjadi tanah yang sunyi sepi. Maka tahulah kamu bahwa Akulah TUHAN." TUHAN berkata, "Hai raja Mesir! Karena engkau mengatakan bahwa Sungai Nil adalah milikmu dan bahwa engkaulah yang membuatnya,
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 maka Aku menjadi musuhmu, dan musuh Sungai Nilmu. Seluruh Mesir akan Kujadikan tanah yang sunyi sepi mulai dari kota Migdol di utara sampai ke kota Aswan di selatan, hingga perbatasan Sudan.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 Tak ada manusia atau binatang yang akan melaluinya. Selama empat puluh tahun tak akan ada orang yang mendiaminya.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 Aku akan membuat Mesir sunyi sepi sehingga di antara negeri-negeri sepi lainnya, Mesirlah yang paling sepi. Selama empat puluh tahun kota-kota di Mesir akan merupakan puing-puing yang jauh lebih parah daripada puing-puing kota mana pun juga. Bangsa Mesir akan Kujadikan pengungsi-pengungsi. Mereka akan tersebar ke segala negeri dan tinggal di tengah-tengah bangsa lain."
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 TUHAN Yang Mahatinggi berkata, "Hai bangsa Mesir, sehabis empat puluh tahun itu, kamu akan Kubawa kembali dari negeri-negeri di tempat kamu telah tersebar.
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 Kamu akan Kupulihkan dan Kusuruh tinggal di Mesir bagian selatan, tanah asalmu. Di sana kamu akan membentuk kerajaan yang lemah,
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 yang paling lemah di seluruh dunia. Aku akan membuat kamu sangat lemah sehingga kamu tak akan dapat memerintah bangsa-bangsa lain ataupun menyombongkan diri terhadap mereka.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 Israel tidak lagi akan meminta bantuan kepadamu. Nasibmu hai bangsa Mesir akan mengingatkan Israel betapa kelirunya mengandalkan Mesir, seperti yang pernah dilakukannya. Maka tahulah Israel bahwa Akulah TUHAN Yang Mahatinggi."
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 Pada tanggal satu bulan satu dalam tahun kedua puluh tujuh masa pembuangan kami, TUHAN berkata kepadaku,
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 "Hai manusia fana, Raja Nebukadnezar dari Babel melancarkan serangan terhadap Tirus. Ia menyuruh prajurit-prajurit memikul beban-beban yang begitu berat, sehingga kepala mereka menjadi botak dan bahu mereka lecet, tetapi baik raja maupun tentaranya tidak mendapat hasil apa pun dengan jerih payah itu.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Sebab itu, Aku TUHAN Yang Mahatinggi berkata: Tanah Mesir akan Kuberikan kepada Raja Nebukadnezar. Ia akan merampok dan merampas serta mengangkut semua kekayaan Mesir sebagai upah bagi tentaranya.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 Tanah Mesir Kuberikan kepadanya sebagai imbalan jasa-jasanya, sebab tentaranya telah bekerja untuk-Ku. Aku, TUHAN Yang Mahatinggi telah berbicara.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 Bilamana hal itu terjadi, Aku akan menjadikan Israel bangsa yang kuat, dan memungkinkan engkau Yehezkiel, berbicara dengan bebas sehingga semua orang dapat mendengar engkau. Maka tahulah mereka bahwa Akulah TUHAN."
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Yehezkiel 29 >