< Ulangan 4 >

1 Lalu Musa berkata kepada bangsa itu, "Taatilah semua hukum yang saya ajarkan kepadamu, supaya kamu boleh hidup sampai mendiami tanah yang akan diberikan TUHAN, Allah leluhurmu, kepadamu.
To, ku ji, ya Isra’ila, ku kasa kunne ga ƙa’idodi da dokokin da nake shirin koya muku. Ku bi su domin ku yi tsawon rai, ku kuma shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku yake ba ku.
2 Apa yang saya perintahkan, jangan ditambah atau dikurangi sedikit pun. Taatilah perintah-perintah TUHAN Allahmu yang saya berikan kepadamu.
Kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin abin da nake umarce ku. Amma ku kiyaye umarnan nan na Ubangiji Allahnku, da na ba ku.
3 Kamu melihat sendiri apa yang dilakukan TUHAN Allahmu di Gunung Peor. Setiap orang yang menyembah Baal di tempat itu dibinasakan-Nya,
Da idanunku, kun ga abin da Ubangiji ya yi a Ba’al-Feyor. Yadda Ubangiji Allahnku ya hallaka waɗansu daga cikinku waɗanda suka yi wa Ba’al-Feyor sujada,
4 sedangkan kamu yang tetap setia kepada TUHAN Allahmu masih hidup sampai sekarang.
Amma ku da kuka manne ga Ubangiji Allahnku, kuna da rai har wa yau.
5 Semua hukum itu saya ajarkan kepadamu seperti yang diperintahkan TUHAN Allahku. Taatilah kesemuanya itu di negeri yang akan kamu masuki dan diami itu.
Ga shi, na koya muku ƙa’idodi da dokoki, yadda Ubangiji Allahna ya umarce ni, don ku bi su a ƙasar da za ku shiga ku mallaki.
6 Lakukanlah itu dengan setia. Kalau kamu berbuat demikian, maka kebijaksanaanmu menjadi nyata bagi bangsa-bangsa lain. Apabila mereka mendengar tentang hukum-hukum itu, mereka akan berkata, 'Alangkah bijaksana dan cerdasnya bangsa yang besar itu!'
Ku kiyaye su, ku aikata su, gama yin haka zai tabbatar wa sauran al’ummai, kuna da hikima da ganewa. Sa’ad da al’ummai za su ji waɗannan dokoki, za su ce, “Ba shakka, wannan babbar al’umma tana da hikima da ganewa.”
7 Bangsa besar manakah yang mempunyai ilah yang begitu dekat apabila diperlukan seperti TUHAN Allah kita dekat kepada kita? Ia menjawab kapan saja kita berseru minta tolong kepada-Nya.
Wace al’umma ce mai girma haka wadda allolinta take kusa da su yadda Ubangiji Allahnmu yake kusa da mu a duk sa’ad da muka yi addu’a gare shi?
8 Dan bangsa besar manakah yang mempunyai hukum-hukum yang begitu adil seperti hukum-hukum yang saya ajarkan kepadamu hari ini?
Wace al’umma ce mai girma haka wadda take da ƙa’idodi da dokoki masu adalci kamar waɗannan ƙunshin dokokin da nake sa a gabanku a yau?
9 Perhatikanlah dan ingatlah baik-baik, supaya seumur hidupmu kamu tidak lupa apa yang sudah kamu saksikan sendiri. Ceritakanlah kepada anak-cucumu
Ku kula, ku kuma lura da kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da idanunku suka gani, ko kuwa ku bari su fita daga zuciyarku muddin ranku. Ku koyar da su ga’ya’yanku, da’ya’yan’ya’yanku.
10 tentang hari itu, ketika kamu berdiri di depan TUHAN Allahmu di Gunung Sinai. Pada waktu itu Ia berkata kepadaku, 'Kumpulkanlah bangsa itu. Aku ingin mereka mendengar apa yang hendak Kusampaikan, supaya mereka belajar taat kepada-Ku seumur hidup, dan supaya mereka mengajar anak-anak mereka untuk taat kepada-Ku.'
Ku tuna da ranar da kuka tsaya a gaban Ubangiji Allahnku a Horeb, sa’ad da ya ce mini, “Ka tara mutane a gabana, don su ji maganata, su koya yin mini bangirma muddin ransu a ƙasar, su kuma iya koyar da su ga’ya’yansu.”
11 Ceritakanlah kepada anak-anakmu bagaimana kamu datang dan berdiri di kaki gunung yang diliputi asap gelap seperti awan tebal dan apinya menyala sampai ke langit.
Sai kuka matso kusa, kuka tsaya a gindin dutse yayinda yana cin wuta har zuwa sararin sama, ga kuma baƙin gizagizai da kuma baƙin duhu.
12 Kemudian TUHAN berbicara kepadamu dari api dan kamu mendengar suara-Nya, tetapi tidak melihat-Nya dalam bentuk apa pun.
Sai Ubangiji ya yi magana daga wutar. Kuka ji furcin kalmomin, amma ba ku ga siffar kome ba, sai dai murya kaɗai kuka ji.
13 Di sana Ia memaklumkan kepadamu apa yang harus kamu lakukan untuk menepati perjanjian yang dibuat-Nya dengan kamu. Sepuluh Perintah yang telah ditulis-Nya pada kedua batu tulis itu harus kamu lakukan.
Ya furta alkawarinsa gare ku, Dokoki Goma, waɗanda ya umarce ku ku bi, ya kuma rubuta su a alluna biyu.
14 TUHAN menyuruh saya mengajarkan kepadamu semua hukum yang harus ditaati di negeri yang nanti kamu masuki dan diami itu."
Sa’an nan Ubangiji ya umarce ni a wannan lokaci, in koya muku ƙa’idodi da dokokin da za ku bi a ƙasar da kuke hayewa Urdun don mallake.
15 "Ingatlah baik-baik! Ketika TUHAN berbicara kepadamu dari dalam api di Gunung Sinai, kamu tidak melihat apa-apa.
Ba ku ga wata siffa a ranar da Ubangiji ya yi magana da ku a Horeb daga wuta ba. Saboda haka ku lura da kanku sosai,
16 Jadi jagalah supaya kamu jangan sampai berdosa karena membuat bagi dirimu sendiri patung untuk disembah dalam bentuk apa pun, laki-laki atau perempuan,
don kada ku lalace, ku kuma yi wa kanku gunki, siffa ta wani kama, ko a kamannin namiji, ko kuwa ta mace,
17 burung atau ikan, binatang melata atau binatang lainnya.
ko a kamannin wata dabba a duniya, ko na wani tsuntsun da yake tashi a sama,
ko kuwa a kamannin wata halittar da take rarrafe a ƙasa, ko na wani kifi a cikin ruwaye a ƙarƙashi.
19 Janganlah berdosa karena menyembah dan mengabdi kepada apa yang kamu lihat di langit: matahari, bulan dan bintang-bintang. TUHAN Allahmu membiarkan bangsa-bangsa lain menyembah benda-benda itu.
Sa’ad da kuka ɗaga ido kuka kali sama, kuka ga rana da wata, da taurari, da dukan halittun sama, sai ku kula fa, kada ku jarrabtu, ku ce za ku yi musu sujada, ko ku bauta musu; abubuwan nan Ubangiji Allahnku ne ya rarraba wa dukan al’umman da suke ko’ina a ƙarƙashin sararin sama.
20 Tetapi kamu adalah bangsa yang diselamatkan-Nya dari Mesir, tempat kamu menderita dengan hebat. Kamu dibawa-Nya keluar dari negeri itu, supaya menjadi bangsa-Nya sendiri seperti keadaanmu sekarang ini.
Amma ku, Ubangiji ya ɗauke ku, ya fid da ku daga matuya mai narken ƙarfe, wato, daga Masar, domin ku zama jama’arsa ta musamman kamar yadda kuke a yau.
21 Tetapi TUHAN Allahmu menjadi marah kepada saya oleh karena kamu, dan Ia bersumpah bahwa saya tak akan menyeberangi Sungai Yordan untuk masuk ke tanah subur yang akan diberikan-Nya kepadamu.
Ubangiji ya yi fushi da ni saboda ku, ya kuma yi rantsuwa cewa ba zan haye Urdun, in shiga ƙasan nan mai kyau da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo ba.
22 Tak lama lagi kamu akan menyeberang dan menduduki tanah yang subur itu; tetapi saya tidak ikut, sebab saya akan mati di sini.
Zan mutu a wannan ƙasa; ba zan haye Urdun ba; amma kuna gab da ƙetarewa, ku mallaki wannan ƙasa mai kyau.
23 Ingatlah baik-baik! Jangan lupa akan perjanjian yang dibuat TUHAN Allahmu dengan kamu. Taatilah perintah-Nya; jangan sekali-kali membuat bagi dirimu patung dalam bentuk apa pun untuk disembah,
Ku yi hankali kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku; kada fa ku yi wa kanku gunki a kamannin wani abin da Ubangiji Allahnku ya hana.
24 sebab TUHAN Allahmu seperti api yang menghanguskan. Ia tak mau disamakan dengan apa pun.
Gama Ubangiji Allahnku wuta ne mai ƙuna, Allah ne mai kishi.
25 Juga kalau kamu nanti sudah lama tinggal di negeri itu dan sudah beranak cucu, jangan berdosa karena membuat bagi dirimu patung dalam bentuk apa saja. Perbuatan itu suatu kejahatan di mata TUHAN Allahmu dan akan membuat Ia marah.
Bayan kun haifi’ya’ya da jikoki, kuka kuma zauna na dogon lokaci a ƙasar, in har kuka lalace, kuka kuma yi wani irin gunki, kuna aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnku, kuna kuma sa shi fushi.
26 Kiranya langit dan bumi hari ini menjadi saksi bahwa kalau kamu tidak taat kepada saya, kamu akan segera lenyap dari tanah yang kamu diami di seberang Sungai Yordan itu. Kamu tak akan lama tinggal di situ; kamu akan dibinasakan sama sekali.
Yau, na kira sama da duniya, su zama shaidata a kanku. Idan kuka yi rashin biyayya, lalle za ku hallaka nan da nan daga ƙasar da kuke ƙetare Urdun ku gāda. Ba za ku daɗe a cikinta ba, amma za a kawar da ku ƙaƙaf.
27 TUHAN akan menceraiberaikan kamu di antara bangsa-bangsa lain dan hanya sedikit di antara kamu yang tetap hidup.
Ubangiji zai watsar da ku a cikin mutane, ɗan kaɗan ne kaɗai za su ragu a cikin al’umman da Ubangiji zai kai ku.
28 Di situ kamu akan berbakti kepada ilah-ilah yang dibuat dengan tangan manusia, ilah-ilah dari kayu dan batu yang tidak dapat melihat atau mendengar, tidak dapat makan atau mencium.
A can za ku bauta wa allolin da mutum ya yi, na itace da dutse da ba sa gani, ba sa ji, ba sa ci, ba kuma iya sansanawa.
29 Lalu kamu akan mencari TUHAN Allahmu, dan kalau kamu mencari-Nya dengan segenap hatimu, kamu akan menemukan Dia.
Amma daga can in kuka nemi Ubangiji Allahnku, da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, za ku same shi.
30 Apabila kamu ditimpa semua bencana itu dan kamu ada dalam kesukaran, maka kamu akan kembali kepada TUHAN Allahmu dan taat kepada-Nya.
Sa’ad da kuke cikin wahala saboda waɗannan abubuwan da suka same ku nan gaba, to, sai ku juyo ga Ubangiji Allahnku, ku kuma yi masa biyayya.
31 TUHAN Allahmu adalah Allah yang sangat berbelaskasihan. Ia tak akan meninggalkan atau membinasakan kamu, atau melupakan perjanjian yang dibuat-Nya sendiri dengan leluhurmu.
Gama Ubangiji Allahnku, Allah ne mai jinƙai; ba zai yashe ku ko yă hallaka, ko kuma yă manta da alkawarin da ya yi da kakanninku, wanda ya tabbatar da su da rantsuwa ba.
32 Selidikilah masa lampau, jauh sebelum kamu lahir, mulai dari hari ketika Allah menciptakan manusia di bumi ini. Carilah di seluruh muka bumi. Pernahkah hal sehebat ini terjadi sebelumnya? Pernahkah ada orang yang mendengar tentang kejadian semacam ini?
Ku bincika dukan tarihi mana, tun daga lokacin da Allah ya halicci mutane a cikin duniya har yă zuwa yanzu; ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?
33 Pernahkah ada bangsa yang tetap hidup setelah mendengar suatu ilah berbicara kepada mereka dari api, seperti yang kamu alami?
Akwai waɗansu mutanen da suka taɓa jin muryar Allah yana magana daga wuta, kamar yadda kuka ji har suka rayu?
34 Pernahkah ada suatu ilah yang berani mengambil suatu bangsa dari bangsa-bangsa yang ada lalu menjadikan mereka umatnya sendiri, seperti yang dilakukan TUHAN Allahmu untukmu di Mesir? Kamu lihat sendiri bagaimana Allah dengan kekuatan yang besar mendatangkan bencana dan perang, mengerjakan keajaiban-keajaiban dan melakukan hal-hal yang dahsyat.
Akwai wani allahn da ya taɓa yin ƙoƙari yă ɗauko wa kansa wata al’umma daga wata al’umma, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu masu banmamaki da al’ajabai, ta wurin yaƙi, ta wurin hannu mai iko, da kuma hannu mai ƙarfi, ko kuwa ta wurin ayyuka masu bangirma da na banmamaki, kamar dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi saboda ku a Masar, a kan idanunku?
35 Semua itu ditunjukkan TUHAN kepadamu untuk membuktikan bahwa hanya TUHAN itu Allah, dan tidak ada yang lain.
An nuna muku dukan waɗannan abubuwa saboda ku san cewa Ubangiji, shi ne Allah; ban da shi, babu wani.
36 Dari langit Ia memperdengarkan suara-Nya kepadamu untuk mengajar kamu; di bumi ini Ia telah memperlihatkan kepadamu api-Nya yang hebat, dan dari api itu Ia berbicara kepadamu.
Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, don yă hore ku. A duniya ya nuna muku wutarsa mai girma, kuka kuma ji kalmominsa daga wuta.
37 Karena Ia mencintai leluhurmu, maka kamu telah dipilih-Nya; dengan kuasa-Nya yang besar kamu telah dibawa-Nya keluar dari Mesir.
Domin ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓi zuriyarsu a bayansu, ya fitar da ku daga Masar ta wurin kasancewarsa da kuma ƙarfinsa mai girma,
38 Bangsa-bangsa yang lebih besar dan lebih kuat diusir-Nya dari hadapanmu, untuk mengantar kamu ke negeri mereka yang diberikan-Nya kepadamu, negeri yang sekarang menjadi milikmu.
don yă fitar da ku a gaban al’ummai da suka fi ku girma da kuma ƙarfi, ya kawo ku cikin ƙasarsu, don yă ba ku ita ta zama gādonku, kamar yadda yake a yau.
39 Sebab itu sadarilah hari ini dan jangan lupa: TUHAN satu-satunya Allah di langit dan di bumi; tak ada yang lain.
Ku sani, ku kuma riƙe a zuciya a wannan rana, cewa Ubangiji shi ne Allah a sama da kuma a ƙasa. Babu wani kuma.
40 Taatilah semua hukum yang saya berikan kepadamu hari ini, maka kamu dan keturunanmu akan sejahtera dan terus hidup di negeri yang diberikan TUHAN Allahmu menjadi milikmu untuk selama-lamanya."
Ku kiyaye ƙa’idodi da umarnai, waɗanda nake ba ku a yau, domin zaman lafiyarku da kuma na zuriyarku bayan ba ku, domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku har abada.
41 Lalu Musa menunjuk tiga kota di sebelah timur Sungai Yordan
Sa’an nan Musa ya keɓe birane uku gabas da Urdun,
42 menjadi kota suaka, tempat orang dapat menyelamatkan diri kalau ia dengan tidak sengaja telah membunuh orang yang bukan musuhnya. Ia dapat melarikan diri ke salah satu kota itu supaya tidak dibunuh juga.
waɗanda duk wanda ya yi kisankai, in ba da gangan ba ne ya kashe maƙwabcinsa, wanda babu ƙiyayya tsakaninsu a dā, zai iya gudu zuwa. Zai iya gudu zuwa cikin ɗaya daga waɗannan birane, yă tsira da ransa.
43 Untuk suku Ruben disediakan kota Bezer di dataran tinggi padang gurun; untuk suku Gad kota Ramot di daerah Gilead, dan untuk orang Manasye kota Golan di daerah Basan.
Biranen kuwa su ne, Bezer a dutsen hamada, don mutanen Ruben; Ramot Gileyad, don mutanen Gad; da kuma Golan a Bashan, don mutanen Manasse.
44 Lalu Musa memberi hukum-hukum dan peraturan-peraturan Allah kepada bangsa Israel.
Wannan ita ce dokar da Musa ya sa a gaban Isra’ilawa.
45 Hal itu dilakukannya sesudah mereka keluar dari Mesir dan berada di lembah sebelah timur Sungai Yordan, berhadapan dengan kota Bet-Peor. Wilayah itu bekas daerah Sihon, raja orang Amori, yang dahulu memerintah di kota Hesybon. Musa dan bangsa Israel mengalahkan dia pada waktu mereka keluar dari Mesir.
Waɗannan su ne farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Musa ya ba su, sa’ad da suka fito daga Masar.
Sa’ad da suke a kwari kusa da Bet-Feyor, gabas da Urdun, a ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, da Musa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi sa’ad da suka fito daga Masar.
47 Mereka menduduki tanah Raja Sihon itu, juga tanah Raja Og dari Basan, seorang raja Amori lain yang tinggal di sebelah timur Sungai Yordan.
Suka mallaki ƙasarsa da kuma ƙasar Og sarkin Bashan, sarakuna biyu na Amoriyawa, gabas da Urdun.
48 Tanah itu terbentang dari kota Aroer di tepi Sungai Arnon, terus ke utara sampai Gunung Siryon, yaitu Gunung Hermon,
Wannan ƙasa ta tashi daga Arower a kewayen Kwarin Arnon zuwa Dutsen Siyon (wato, Hermon),
49 dan seluruh daerah di sebelah timur Sungai Yordan ke selatan sampai Laut Mati di kaki Gunung Pisga.
ya kuma haɗa da dukan Araba gabas da Urdun, har zuwa tekun Araba a gindin gangaren Fisga.

< Ulangan 4 >