< Ulangan 27 >

1 Kemudian bersama para pemimpin Israel, Musa menyampaikan pesan ini kepada bangsa itu, "Taatilah segala perintah yang saya berikan kepadamu hari ini.
Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
2 Pada hari kamu menyeberangi Sungai Yordan untuk masuk ke negeri yang diberikan TUHAN Allahmu kepadamu, kamu harus menegakkan beberapa batu besar lalu mengapurnya.
Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
3 Tuliskanlah pada batu-batu itu setiap perkataan dari hukum-hukum ini. Apabila kamu sudah masuk ke negeri yang kaya dan subur yang dijanjikan TUHAN, Allah nenek moyangmu kepadamu,
Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
4 dan kamu sudah ada di seberang Sungai Yordan, kamu harus pergi ke Gunung Ebal. Di situ kamu harus menegakkan dan mengapur batu-batu itu seperti yang saya perintahkan kepadamu hari ini.
Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
5 Di tempat itu harus juga kamu dirikan bagi TUHAN Allahmu sebuah mezbah dari batu-batu yang belum pernah dikerjakan dengan alat-alat besi,
Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
6 sebab setiap mezbah yang didirikan untuk TUHAN Allahmu harus dibuat dari batu yang utuh. Di atas mezbah itu kamu harus mempersembahkan kurban-kurban bakaran.
Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
7 Persembahkanlah juga kurban perdamaianmu dan makanlah di situ serta bersukacitalah di hadapan TUHAN Allahmu.
Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
8 Di atas batu-batu yang dikapur itu harus kamu tulis dengan jelas setiap perkataan dari hukum-hukum Allah."
Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
9 Kemudian bersama para imam Lewi, Musa berkata kepada seluruh bangsa Israel, "Saudara-saudara, perhatikanlah dan dengarlah! Hari ini kamu sudah menjadi umat TUHAN Allahmu.
Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
10 Sebab itu taatilah TUHAN Allahmu dan lakukanlah semua perintah-Nya yang saya berikan kepadamu hari ini."
Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
11 Lalu Musa berkata kepada bangsa Israel,
A wannan rana Musa ya umarce mutane,
12 "Sesudah kamu menyeberangi Sungai Yordan, suku Simeon, Lewi, Yehuda, Isakhar, Yusuf dan Benyamin harus berdiri di atas Gunung Gerizim pada waktu diucapkan berkat atas bangsa ini.
Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
13 Pada waktu diucapkan kutuk, suku Ruben, Gad, Asyer, Zebulon, Dan serta Naftali harus berdiri di atas Gunung Ebal.
Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
14 Orang-orang Lewi harus mengucapkan kata-kata berikut ini dengan suara nyaring dan orang Israel harus menjawab, 'Amin'.
Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
15 Orang-orang Lewi: 'Terkutuklah orang yang membuat patung dari batu, kayu atau logam, dan menyembahnya dengan sembunyi-sembunyi; TUHAN membenci pemujaan berhala!' Seluruh rakyat: 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
16 'Terkutuklah orang yang tidak menghormati orang tuanya dan membiarkan mereka terlantar.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
17 'Terkutuklah orang yang menggeser batas tanah tetangganya.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
18 'Terkutuklah orang yang menyesatkan orang buta.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
19 'Terkutuklah orang yang merampas hak orang asing, anak yatim piatu dan janda.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
20 'Terkutuklah orang yang menghina ayahnya karena bersetubuh dengan salah seorang istri ayahnya.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
21 'Terkutuklah orang yang bersetubuh dengan binatang.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
22 'Terkutuklah orang yang bersetubuh dengan saudaranya perempuan yang sekandung, atau saudaranya seayah atau seibu.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
23 'Terkutuklah orang yang bersetubuh dengan ibu mertuanya.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
24 'Terkutuklah orang yang melakukan pembunuhan dengan sembunyi-sembunyi.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
25 'Terkutuklah orang yang menerima suap untuk membunuh orang yang tidak bersalah.' 'Amin!'
“La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
26 'Terkutuklah orang yang tidak menepati hukum dan ajaran Allah dengan perbuatan.' 'Amin!'"
“La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”

< Ulangan 27 >