< विलापगीत 3 >

1 उसके रोष की छड़ी से दुःख भोगनेवाला पुरुष मैं ही हूँ;
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 वह मुझे ले जाकर उजियाले में नहीं, अंधियारे ही में चलाता है;
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 उसका हाथ दिन भर मेरे ही विरुद्ध उठता रहता है।
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 उसने मेरा माँस और चमड़ा गला दिया है, और मेरी हड्डियों को तोड़ दिया है;
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 उसने मुझे रोकने के लिये किला बनाया, और मुझ को कठिन दुःख और श्रम से घेरा है;
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 उसने मुझे बहुत दिन के मरे हुए लोगों के समान अंधेरे स्थानों में बसा दिया है।
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 मेरे चारों ओर उसने बाड़ा बाँधा है कि मैं निकल नहीं सकता; उसने मुझे भारी साँकल से जकड़ा है;
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 मैं चिल्ला-चिल्ला के दुहाई देता हूँ, तो भी वह मेरी प्रार्थना नहीं सुनता;
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 मेरे मार्गों को उसने गढ़े हुए पत्थरों से रोक रखा है, मेरी डगरों को उसने टेढ़ी कर दिया है।
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 १० वह मेरे लिये घात में बैठे हुए रीछ और घात लगाए हुए सिंह के समान है;
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 ११ उसने मुझे मेरे मार्गों से भुला दिया, और मुझे फाड़ डाला; उसने मुझ को उजाड़ दिया है।
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 १२ उसने धनुष चढ़ाकर मुझे अपने तीर का निशाना बनाया है।
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 १३ उसने अपनी तीरों से मेरे हृदय को बेध दिया है;
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 १४ सब लोग मुझ पर हँसते हैं और दिन भर मुझ पर ढालकर गीत गाते हैं,
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 १५ उसने मुझे कठिन दुःख से भर दिया, और नागदौना पिलाकर तृप्त किया है।
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 १६ उसने मेरे दाँतों को कंकड़ से तोड़ डाला, और मुझे राख से ढाँप दिया है;
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 १७ और मुझ को मन से उतारकर कुशल से रहित किया है; मैं कल्याण भूल गया हूँ;
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 १८ इसलिए मैंने कहा, “मेरा बल नष्ट हुआ, और मेरी आशा जो यहोवा पर थी, वह टूट गई है।”
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 १९ मेरा दुःख और मारा-मारा फिरना, मेरा नागदौने और विष का पीना स्मरण कर!
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 २० मैं उन्हीं पर सोचता रहता हूँ, इससे मेरा प्राण ढला जाता है।
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 २१ परन्तु मैं यह स्मरण करता हूँ, इसलिए मुझे आशा है:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 २२ हम मिट नहीं गए; यह यहोवा की महाकरुणा का फल है, क्योंकि उसकी दया अमर है।
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 २३ प्रति भोर वह नई होती रहती है; तेरी सच्चाई महान है।
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 २४ मेरे मन ने कहा, “यहोवा मेरा भाग है, इस कारण मैं उसमें आशा रखूँगा।”
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 २५ जो यहोवा की बाट जोहते और उसके पास जाते हैं, उनके लिये यहोवा भला है।
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 २६ यहोवा से उद्धार पाने की आशा रखकर चुपचाप रहना भला है।
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 २७ पुरुष के लिये जवानी में जूआ उठाना भला है।
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 २८ वह यह जानकर अकेला चुपचाप रहे, कि परमेश्वर ही ने उस पर यह बोझ डाला है;
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 २९ वह अपना मुँह धूल में रखे, क्या जाने इसमें कुछ आशा हो;
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 ३० वह अपना गाल अपने मारनेवाले की ओर फेरे, और नामधराई सहता रहे।
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 ३१ क्योंकि प्रभु मन से सर्वदा उतारे नहीं रहता,
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 ३२ चाहे वह दुःख भी दे, तो भी अपनी करुणा की बहुतायत के कारण वह दया भी करता है;
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 ३३ क्योंकि वह मनुष्यों को अपने मन से न तो दबाता है और न दुःख देता है।
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 ३४ पृथ्वी भर के बन्दियों को पाँव के तले दलित करना,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 ३५ किसी पुरुष का हक़ परमप्रधान के सामने मारना,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 ३६ और किसी मनुष्य का मुकद्दमा बिगाड़ना, इन तीन कामों को यहोवा देख नहीं सकता।
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 ३७ यदि यहोवा ने आज्ञा न दी हो, तब कौन है कि वचन कहे और वह पूरा हो जाए?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 ३८ विपत्ति और कल्याण, क्या दोनों परमप्रधान की आज्ञा से नहीं होते?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 ३९ इसलिए जीवित मनुष्य क्यों कुड़कुड़ाए? और पुरुष अपने पाप के दण्ड को क्यों बुरा माने?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 ४० हम अपने चाल चलन को ध्यान से परखें, और यहोवा की ओर फिरें!
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 ४१ हम स्वर्ग में वास करनेवाले परमेश्वर की ओर मन लगाएँ और हाथ फैलाएँ और कहें:
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 ४२ “हमने तो अपराध और बलवा किया है, और तूने क्षमा नहीं किया।
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 ४३ तेरा कोप हम पर है, तू हमारे पीछे पड़ा है, तूने बिना तरस खाए घात किया है।
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 ४४ तूने अपने को मेघ से घेर लिया है कि तुझ तक प्रार्थना न पहुँच सके।
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 ४५ तूने हमको जाति-जाति के लोगों के बीच में कूड़ा-करकट सा ठहराया है।
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 ४६ हमारे सब शत्रुओं ने हम पर अपना-अपना मुँह फैलाया है;
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 ४७ भय और गड्ढा, उजाड़ और विनाश, हम पर आ पड़े हैं;
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 ४८ मेरी आँखों से मेरी प्रजा की पुत्री के विनाश के कारण जल की धाराएँ बह रही है।
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 ४९ मेरी आँख से लगातार आँसू बहते रहेंगे,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 ५० जब तक यहोवा स्वर्ग से मेरी ओर न देखे;
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 ५१ अपनी नगरी की सब स्त्रियों का हाल देखने पर मेरा दुःख बढ़ता है।
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 ५२ जो व्यर्थ मेरे शत्रु बने हैं, उन्होंने निर्दयता से चिड़िया के समान मेरा आहेर किया है;
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 ५३ उन्होंने मुझे गड्ढे में डालकर मेरे जीवन का अन्त करने के लिये मेरे ऊपर पत्थर लुढ़काए हैं;
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 ५४ मेरे सिर पर से जल बह गया, मैंने कहा, ‘मैं अब नाश हो गया।’
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 ५५ हे यहोवा, गहरे गड्ढे में से मैंने तुझ से प्रार्थना की;
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 ५६ तूने मेरी सुनी कि जो दुहाई देकर मैं चिल्लाता हूँ उससे कान न फेर ले!
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 ५७ जब मैंने तुझे पुकारा, तब तूने मुझसे कहा, ‘मत डर!’
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 ५८ हे यहोवा, तूने मेरा मुकद्दमा लड़कर मेरा प्राण बचा लिया है।
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 ५९ हे यहोवा, जो अन्याय मुझ पर हुआ है उसे तूने देखा है; तू मेरा न्याय चुका।
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 ६० जो बदला उन्होंने मुझसे लिया, और जो कल्पनाएँ मेरे विरुद्ध की, उन्हें भी तूने देखा है।
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 ६१ हे यहोवा, जो कल्पनाएँ और निन्दा वे मेरे विरुद्ध करते हैं, वे भी तूने सुनी हैं।
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 ६२ मेरे विरोधियों के वचन, और जो कुछ भी वे मेरे विरुद्ध लगातार सोचते हैं, उन्हें तू जानता है।
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 ६३ उनका उठना-बैठना ध्यान से देख; वे मुझ पर लगते हुए गीत गाते हैं।
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 ६४ हे यहोवा, तू उनके कामों के अनुसार उनको बदला देगा।
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 ६५ तू उनका मन सुन्न कर देगा; तेरा श्राप उन पर होगा।
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 ६६ हे यहोवा, तू अपने कोप से उनको खदेड़-खदेड़कर धरती पर से नाश कर देगा।”
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< विलापगीत 3 >