< לוּקָס 1 >

אחרי אשר רבים הואילו לחבר ספור המעשים אשר נאמנו בשלמות בתוכנו׃ 1
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
כאשר מסרום לנו הראים אתם בעיניהם מתחלה ואשר היו משרתי הדבר׃ 2
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
חשבתי לטוב גם אני החפש כל הדברים היטב מראשיתם לכתבם אליך בסדר תאופילוס האדיר׃ 3
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
למען תדע קשט האמרים אשר חנכת בם׃ 4
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
כהן היה בימי הורדוס מלך יהודה זכריה שמו ממשמרת אביה ולו אשה מבנות אהרן ושמה אלישבע׃ 5
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
ושניהם היו צדיקים לפני האלהים והלכי תם בכל מצות יהוה ובחקתיו׃ 6
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
ולא היה להם ילד כי אלישבע עקרה ושניהם באו בימים׃ 7
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
ויהי היום ויכהן לפני אלהים בסדר משמרתו׃ 8
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
וכמשפט עבודת הכהנים יצא גורלו להקטיר קטרת ויבא אל היכל יהוה׃ 9
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
וכל קהל העם היו מתפללים בחוץ בעת הקטרת׃ 10
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
וירא אליו מלאך יהוה עמד לימין מזבח הקטרת׃ 11
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
ויבהל זכריה בראותו אתו ואימה נפלה עליו׃ 12
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
ויאמר אליו המלאך אל תירא זכריהו כי נשמעה תפלתך ואלישבע אשתך תלד לך בן וקראת שמו יוחנן׃ 13
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
והיה לך לשמחה וגיל ורבים ישמחו בהולדו׃ 14
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
כי גדול יהיה לפני יהוה ויין ושכר לא ישתה ורוח הקדש ימלא בעודנו בבטן אמו׃ 15
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
ורבים מבני ישראל ישיב אל יהוה אלהיהם׃ 16
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
והוא ילך לפניו ברוח אליהו ובגבורתו להשיב את לב אבות על בנים ואת הסוררים לתבונת הצדיקים להעמיד ליהוה עם מתקן׃ 17
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
ויאמר זכריה אל המלאך במה אדע זאת כי אני זקנתי ואשתי באה בימים׃ 18
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
ויען המלאך ויאמר אליו אני גבריאל העומד לפני האלהים ושלוח אנכי לדבר אליך ולבשרך את זאת׃ 19
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
והנה תאלם ולא תוכל לדבר עד היום אשר תהיה זאת תחת כי לא האמנת בדברי אשר ימלאו למועדם׃ 20
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
והעם היה מחכה לזכריה ויתמהו כי אחר בהיכל׃ 21
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
ויהי בצאתו לא יכל לדבר אליהם וידעו כי מראה ראה בהיכל וירמז להם ועודנו נאלם׃ 22
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
ויהי כאשר מלאו ימי עבדתו וילך לו אל ביתו׃ 23
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
ויהי אחרי הימים האלה ותהר אלישבע אשתו ותתחבא חמשה חדשים ותאמר׃ 24
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
ככה עשה לי יהוה בימי פקדו אותי לאסף את חרפתי בתוך בני אדם׃ 25
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
ויהי בחדש הששי וישלח המלאך גבריאל מאת האלהים גלילה אל עיר אשר שמה נצרת׃ 26
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
אל בתולה מארשה לאיש אשר שמו יוסף מבית דוד ושם הבתולה מרים׃ 27
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
ויבא המלאך אליה החדרה ויאמר שלום לך אשת חן יהוה עמך ברוכה את בנשים׃ 28
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
והיא בראותה נבהלה לדברו ותאמר בלבה מה היא הברכה הזאת׃ 29
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
ויאמר לה המלאך אל תיראי מרים כי מצאת חן לפני האלהים׃ 30
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
והנך הרה וילדת בן וקראת את שמו ישוע׃ 31
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
והוא גדול יהיה ובן עליון יקרא ויהוה אלהים יתן לו את כסא דוד אביו׃ 32
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
ועל בית יעקב ימלך לעולם ועד ולמלכותו אין קץ׃ (aiōn g165) 33
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
ותאמר מרים אל המלאך איך תהיה זאת ואני אינני ידעת איש׃ 34
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
ויען המלאך ויאמר אליה רוח הקדש תבוא עליך וגבורת עליון תצל עליך על כן גם לקדוש הילוד יקרא בן אלהים׃ 35
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
והנה אלישבע קרובתך אשר קראו לה עקרה גם היא הרתה בן בזקנתה וזה לה החדש הששי׃ 36
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
כי לא יפלא מאלהים כל דבר׃ 37
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
ותאמר מרים הנני שפחת יהוה יהי לי כדברך ויצא מאתה המלאך׃ 38
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
ותקם מרים בימים ההם ותמהר ללכת ההרה אל עיר יהודה׃ 39
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
ותבא בית זכריה ותברך את אלישבע׃ 40
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
ויהי כשמע אלישבע את ברכת מרים וירקד הילד במעיה ותמלא אלישבע רוח הקדש׃ 41
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
ותקרא בקול גדול ותאמר ברוכה את בנשים וברוך פרי בטנך׃ 42
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
ומאין לי זאת אשר אם אדני באה אלי׃ 43
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
כי קול ברכתך בא באזני והנה רקד בשמחה הילד במעי׃ 44
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
ואשרי המאמינה כי המלא תמלא אשר דבר לה מאת יהוה׃ 45
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
ותאמר מרים רוממה נפשי את יהוה׃ 46
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
ותגל רוחי באלהי ישעי׃ 47
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
אשר ראה בעני אמתו כי הנה מעתה כל הדרות יאשרוני כי גדלות עשה לי שדי וקדוש שמו׃ 48
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
וחסדו לדור דורים על יראיו׃ 50
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
גבורות עשה בזרעו פזר גאים במזמות לבבם׃ 51
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
הרס נדיבים מכסאותו וירם שפלים׃ 52
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
רעבים מלא טוב ועשירים שלח ריקם׃ 53
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
תמך בישראל עבדו לזכר את רחמיו׃ 54
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
כאשר דבר אל אבותינו לאברהם ולזרעו עד עולם׃ (aiōn g165) 55
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
ותשב מרים עמה כשלשה חדשים ותשב לביתה׃ 56
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
וימלאו ימי אלישבע ללדת ותלד בן׃ 57
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
וישמעו שכניה וקרוביה כי הגדיל יהוה את חסדו עמה וישמחו אתה׃ 58
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
ויהי ביום השמיני ויבאו למול את הילד ויקראו אתו זכריה על שם אביו׃ 59
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
ותען אמו ותאמר לא כי יוחנן יקרא׃ 60
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
ויאמרו אליה אין איש במשפחתך אשר נקרא בשם הזה׃ 61
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
וירמזו אל אביו לדעת מה השם אשר יחפץ להקרא לו׃ 62
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
וישאל לוח ויכתב עליו לאמר יוחנן שמו ויתמהו כלם׃ 63
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
ויפתח פיו ולשונו פתאם וידבר ויברך את האלהים׃ 64
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
ותפל אימה על כל שכניהם ויספר כל הדברים האלה בכל הרי יהודה׃ 65
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
וישימו כל השמעים אל לבם לאמר מה אפוא יהיה הילד הזה ויד יהוה היתה עמו׃ 66
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
וימלא זכריה אביו רוח הקדש וינבא לאמר׃ 67
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
ברוך יהוה אלהי ישראל כי פקד את עמו וישלח לו פדות׃ 68
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
וירם לנו קרן ישועה בבית דוד עבדו׃ 69
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
כאשר דבר בפי נביאיו הקדושים אשר מעולם׃ (aiōn g165) 70
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
ישועה מאיבינו ומיד כל שנאינו׃ 71
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
לעשות חסד עם אבותינו ולזכר את ברית קדשו׃ 72
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
את השבועה אשר נשבע לאברהם אבינו׃ 73
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
להצילנו מיד איבינו ולתתנו לעבדו בלי פחד׃ 74
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
בתמים ובצדקה לפניו כל ימי חיינו׃ 75
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
ואתה הילד נביא עליון תקרא כי לפני יהוה תלך לפנות את דרכיו׃ 76
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
לתת דעת הישועה לעמו בסליחת חטאתיהם׃ 77
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
ברחמי חסד אלהינו אשר בהם פקדנו הנגה ממרום׃ 78
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
להאיר לישבי חשך וצלמות ולהכין את רגלינו אל דרך השלום׃ 79
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
ויגדל הילד ויחזק ברוח ויהי במדברות עד יום הראתו אל ישראל׃ 80
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< לוּקָס 1 >