< לוּקָס 5 >

יום אחד עמד ישוע על חוף הכינרת ובישר את דבר האלוהים. מספר הנוכחים הלך וגדל, עד שהם נדחפו ונדחקו אליו מכל צד. 1
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
ישוע הבחין בשתי סירות ריקות שעגנו ליד החוף. בעלי הסירות, שהיו דייגים במקצועם, רחצו באותו זמן את רשתותיהם. 2
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
ישוע עלה על אחת הסירות, שהייתה של שמעון, וביקש ממנו להרחיק מעט את הסירה מהחוף, כדי שיוכל לשבת בתוכה ולדבר אל הקהל. 3
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
לאחר שסיים ישוע לדבר אל הקהל, פנה אל שמעון ואמר:”השט את הסירה אל מים עמוקים והשלך את הרשתות כדי לדוג.“ 4
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
”רבי, “השיב שמעון,”בלילה האחרון עבדנו קשה מאוד ולא תפסנו כלום. אולם אם אתה אומר לנו להשליך את הרשתות, נעשה כדברך.“ 5
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
הם השליכו את הרשתות לים, והפעם תפסו כל כך הרבה דגים עד שהרשתות היו כבדות מדי והחלו להיקרע! 6
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
הם קראו לעזרתם את חבריהם שבסירה השנייה, ומילאו את שתי הסירות בדגים עד שכמעט טבעו! 7
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
כשראה שמעון פטרוס את הפלא הגדול, נפל על ברכיו לרגלי ישוע ואמר:”אדוני, עזוב אותי לנפשי, כי אני חוטא גדול מדי ואיני ראוי להיות במחיצתך.“ 8
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
שמעון אמר דברים אלה משום שהוא וכל הנוכחים איתו, כולל שותפיו יעקב ויוחנן בני־זַבְדִּי, היו בתדהמה גדולה לנוכח השלל הבלתי רגיל.”אל תפחד.“אמר ישוע לשמעון.”מעתה ואילך תהיה דייג של בני אדם.“ 9
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
לאחר שהשיטו את הסירות לחוף עזבו הכול והלכו אחרי ישוע. 11
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
באחד הכפרים שבהם ביקר ישוע היה אדם נגוע בצרעת. בראותו את ישוע נפל האיש לרגליו והתחנן:”אדוני, אם רק תרצה תוכל לרפא אותי.“ 12
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
ישוע הושיט את ידו, נגע במצורע ואמר:”ודאי שאני רוצה. הירפא!“ומיד נעלמה הצרעת. 13
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
”אל תספר את הדבר לאיש!“ציווה עליו ישוע.”לך מיד אל הכהן והראה לו שנרפאת. אל תשכח לקחת איתך קרבן – כפי שציווה משה על המטוהרים מצרעת – כדי שכולם יראו שנרפאת.“ 14
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
בכל זאת התפשטו השמועות על גבורתו של ישוע במהירות רבה, ואנשים רבים באו להקשיב לדבריו ולהירפא ממחלותיהם. 15
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
אף־על־פי־כן התחמק מהם ישוע לעיתים קרובות והלך למקומות מבודדים כדי להתפלל. 16
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
יום אחד, כשלימד ישוע כמנהגו, התקבצו סביבו בין השאר גם פרושים וסופרים שבאו מכפרי הגליל, מיהודה ומירושלים, וה׳ העניק לו גבורה גדולה לרפא את החולים. 17
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
כעבור זמן קצר הופיעו מספר אנשים שנשאו חולה משותק על אלונקה. הם רצו להביא את החולה לפני ישוע, 18
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
אולם בשל הצפיפות הרבה לא הצליחו לפלס דרך אל תוך הבית. נושאי האלונקה לא נואשו; הם עלו על גג הבית, עקרו כמה רעפים ממקומם והורידו את האלונקה מהגג אל אמצע החדר – לרגלי ישוע. 19
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
כשראה ישוע את אמונתם, אמר לאיש המשותק:”ידידי, נסלחו לך חטאיך!“ 20
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
”למי הוא חושב את עצמו?“שאלו הפרושים והסופרים בלבם.”הוא מחלל את שם האלוהים, רק אלוהים יכול לסלוח על חטאים!“ 21
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
ישוע הבין את מחשבותיהם ולכן השיב להם:”מדוע אתם חושבים שאני מחלל את שם אלוהים? 22
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
מה לדעתכם קל יותר, לומר’נסלחו לך חטאיך‘, או’קום והתהלך‘? 23
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
אני אוכיח לכם כי לבן־האדם יש בארץ סמכות מלאה לסלוח על חטאים!“ישוע פנה אל האיש המשותק ופקד עליו:”קום! קפל את האלונקה שלך ולך הביתה.“ 24
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
מיד קפץ האיש על רגליו לנגד עיניהם, קיפל את האלונקה שלו והלך לביתו כשהוא מהלל את האלוהים. 25
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
כל הנוכחים נדהמו.”היום ראינו פלא גדול“, אמרו ביראה והללו את האלוהים. 26
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
לאחר מכן יצא ישוע מהעיר ופגש בדרך גובה־מכס אחד, לוי שמו, יושב בשער בית־המכס.”בוא והיה תלמיד שלי“, אמר לו ישוע. 27
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
לוי קם על רגליו, עזב הכול מאחוריו והלך אחרי ישוע. 28
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
ערב אחד הכין לוי ארוחה חגיגית לכבוד ישוע והזמין גובי־מכס מהעבודה, ידידים, שכנים וקרובים. 29
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
אולם הדבר לא מצא־חן בעיני הסופרים והפרושים, אשר התלוננו באוזני תלמידיו של ישוע:”איך הוא יכול לאכול ולשתות בחברת החוטאים האלה?“ 30
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
”החולים הם הזקוקים לרופא, לא הבריאים!“השיב להם ישוע. 31
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
”לא באתי לקרוא לצדיקים לחזור בתשובה, כי אם לחוטאים.“ 32
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
הם המשיכו להתלונן ואמרו:”תלמידי יוחנן המטביל צמים לעיתים קרובות ומתפללים, וגם הפרושים נוהגים כך. מדוע אין תלמידיך צמים?“ 33
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
”האם אנשים שמחים צמים?“השיב ישוע.”האם אורחים המוזמנים לחתונה צמים בחגיגת החתן? 34
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
אולם יבוא יום שהחתן יילקח מהם ואז יצומו.“ 35
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
ישוע סיפר להם את המשל הבא:”איש אינו קורע חולצה חדשה כדי לתפור ממנה טלאי על חולצה ישנה. מי שעושה כך לא זו בלבד שהוא מקלקל את החולצה החדשה, אלא שגם אינו יכול ליהנות מהחולצה הישנה, כי הטלאי אינו מתאים. 36
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
”איש אינו שם יין חדש בחביות ישנות ורקובות, מפני שהיין החדש יבקע את החביות, וכך היין יישפך והחביות תיהרסנה. 37
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
יין חדש יש לשים בחביות חדשות. 38
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
אדם הרגיל לשתות יין ישן אינו חפץ לשנות את מנהגו ולשתות יין חדש.’היין הישן מוצא־חן בעיני‘, הוא יאמר, ולא ירצה אפילו לטעום מהיין החדש.“ 39
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< לוּקָס 5 >