< תהילים 71 >

בך-יהוה חסיתי אל-אבושה לעולם 1
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
בצדקתך תצילני ותפלטני הטה-אלי אזנך והושיעני 2
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
היה לי לצור מעון לבוא-- תמיד צוית להושיעני כי-סלעי ומצודתי אתה 3
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
אלהי--פלטני מיד רשע מכף מעול וחומץ 4
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
כי-אתה תקותי אדני יהוה מבטחי מנעורי 5
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
עליך נסמכתי מבטן--ממעי אמי אתה גוזי בך תהלתי תמיד 6
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
כמופת הייתי לרבים ואתה מחסי-עז 7
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
ימלא פי תהלתך כל-היום תפארתך 8
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
אל-תשליכני לעת זקנה ככלות כחי אל-תעזבני 9
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
כי-אמרו אויבי לי ושמרי נפשי נועצו יחדו 10
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
לאמר אלהים עזבו רדפו ותפשוהו כי-אין מציל 11
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
אלהים אל-תרחק ממני אלהי לעזרתי חישה (חושה) 12
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
יבשו יכלו שטני נפשי יעטו חרפה וכלמה--מבקשי רעתי 13
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
ואני תמיד איחל והוספתי על-כל-תהלתך 14
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
פי יספר צדקתך--כל-היום תשועתך כי לא ידעתי ספרות 15
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
אבוא--בגברות אדני יהוה אזכיר צדקתך לבדך 16
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
אלהים למדתני מנעורי ועד-הנה אגיד נפלאותיך 17
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
וגם עד-זקנה ושיבה-- אלהים אל-תעזבני עד-אגיד זרועך לדור לכל-יבוא גבורתך 18
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
וצדקתך אלהים עד-מרום אשר-עשית גדלות אלהים מי כמוך 19
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
אשר הראיתנו (הראיתני) צרות רבות-- ורעות תשוב תחינו (תחיני) ומתהמות הארץ תשוב תעלני 20
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
תרב גדלתי ותסב תנחמני 21
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
גם-אני אודך בכלי-נבל-- אמתך אלהי אזמרה לך בכנור-- קדוש ישראל 22
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
תרננה שפתי כי אזמרה-לך ונפשי אשר פדית 23
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
גם-לשוני-- כל-היום תהגה צדקתך כי-בשו כי-חפרו מבקשי רעתי 24
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< תהילים 71 >