< Luka 5 >

1 EIA kekahi, hookeke ae la ka ahakanaka ia ia, e lohe i ka olelo a ke Akua, i kona ku kokoke ana ma ka moanawai o Genesareta.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Ike aku la ia i na moku elua e ku ana i ka moanawai; aka, ua hele ka poe lawaia mai o laua aku, e kaka ana i ka lakou mau upena.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Ee aku la ia maluna o kekahi o ua mau moku la, no Simona ia, noi mai la hoi ia ia e hoopanee iki aku oia mai ka aina aku; a noho iho la ia ilalo, ao mai la no hoi ia i ka ahakanaka, ma ka moku mai.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 A pau kana olelo ana mai, i ae la oia ia Simona, E neenee aku i kahi hohonu, a e kuu iho i ka oukou mau upena i hookahi hei ana.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 A olelo aku o Simona, i aku la ia ia, E ke Kumu, ua hana makou i ka po nei a ao, aohe mea i loaa; aka, no kau olelo, e kuu iho au i ka upena.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Hana iho la hoi lakou pela, puni iho la ka ia he nui loa, a nahae ae la ka lakou upena.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Peahi aku la lakou i na hoalawehana ma kekahi moku, e holo mai e kokua ia lakou; holo mai la lakou a hoopiha ia mau moku a elua, a kokoke loa e komo.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 A ike ae la o Simona Petero, alaila moe iho la ia ma na kuli o Iesu, i aku la, E hele aku oe mai o'u aku nei, e ka Haku, no ka mea, he kanaka hewa wau.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 No ka mea, ua weliweli iho la ia, o lakou pu a pau kekahi me ia, i ka hei ana o na ia i loaa ia lakou.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Pela hoi o Iakobo, a me Ioane, na keiki a Zebedaio, ko Simona mau hoalawehana. I mai la o Iesu ia Simona, Mai makau oe, no ka mea, mahope aku, e hoohei ae oe i kanaka.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 A hoopae lakou ia mau moku iuka, haalele aku la lakou i na mea a pau, a hahai ia ia.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Eia kekahi, ia ia e noho ana maloko o kekahi o ia mau kulanakauhale, aia hoi, he kanaka paapu i ka lepera; a ike oia ia Iesu, moe iho la ia ilalo ke alo, nonoi aku la ia ia, i aku la, E ka Haku, ina makemake oe, e hiki no ia oe ke hoomaemae ia'u.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Kikoo mai la ko Iesu lima, hoopa iho la ia ia, i mai la, Makemake au, e hoomaemaeia hoi oe. Haalele koke no hoi ka mai lepera ia ia.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Kauoha ae la o Iesu ia ia, mai hai aku ia hai, aka, e hele e hoike ia oe iho i ke kahuna, a e haawi aku hoi i ka mohai no kou maemae ana, e like me ka Mose i kauoha mai ai, i maopopo i kanaka.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Kukui loa ae la kona kaulana, a lulumi mai la na ahakanaka nui, e lohe ia ia, a e hoolaia e ia ko lakou nawaliwali.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Hele aku la ia i na wahi mehameha, a pule iho la.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Eia kekahi, i kekahi la, i kana ao ana, e noho kokoke ana na Parisaio a me na kumu no kanawai, na mea i hele mai, mai na kulanakauhale a pau ma Galilaia a me Iudea mai, a mai Ierusalema mai hoi; a ilaila ka mana o ka Haku e hoola ia lakou.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Aia hoi, lawe mai la na kanaka ma ka moe i kekahi kanaka, i loohia e ka lolo; a huli lakou e hookomo ia ia iloko, a e waiho iho ia ia imua ona.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Aole hoi i loaa ia lakou ke hookomo ia ia, no ka nui o na kanaka, pii ae la lakou iluna o ka hale, a mawaena o na papa lepo pili, i kuu iho ai lakou ia ia ilalo, me ka moe, iwaenakonu imua o Iesu.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 A i kona ike ana i ko lakou manaoio, i mai la oia ia ia, E ke kanaka, ua kalaia na hewa ou.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Hoomaka iho la na Parisaio, a me na kakauolelo e kukakuka, i iho la, Owai la keia e olelo nei i na olelo hoinoino? E hiki la ia wai ke kala i ka hala, anoai o ke Akua no?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Ike iho la o Iesu i ko lakou manao, olelo mai la oia ia lakou, i mai la, No ke aha la oukou e kukakuka nei iloko o ko oukou naau?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Mahea ka uuku ke olelo, Ua kalaia na hewa ou, a, ke olelo paha, e ala, a e hele?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Aka, i ike oukou he mana ko ke Keiki a ke kanaka ma ka honua e kala i ka hala, (olelo ia i ka mea mai lolo, ) Ke olelo aku nei au ia oe, e ala, e kaikai i kou wahi moe, a e hele aku i kou hale.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Ku koke ae la ia imua o lakou, kaikai ae la i kona wahi moe, a hele aku la i kona hale me ka, hoomaikai ana i ke Akua.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Loohia lakou a pau i ka pihoihoi, a hoomaikai aku la i ke Akua, a piha lakou i ka makau, i mai la, Ua ike kakou i na mea kupanaha i keia la.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Mahope iho o ia mau mea, hele ae la ia, a ike iho la ia i ka lunaauhau, o Levi kona inoa, e noho ana i kahi hookupu; i iho la oia ia ia, E hahai mai oe ia'u.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Haalele no ia i na mea a pau, ku ae la, a hahai mamuli ona.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Hana iho la o Levi i ahaaina nui nona iloko o kona hale iho: he nui no ka poe lunaauhau a me na mea e ae i noho pu me lakou.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Aka, ohumu ko laila poe kakauolelo, a me na Parisaio i kana mau haumana, i ae la, No ke aha la oukou e ai pu ai, a e inu pu hoi me na lunaauhau a me na lawehala?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Olelo mai la o Iesu ia lakou, i mai la, Aole no ka poe ola ke kahuna lapaau e pono ai; aka, no ka poe mai uo ia.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Aole ka poe pono ka'u i hele mai nei e ao aku, aka, o ka poe hewa e mihi.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 I aku la lakou ia ia, No ke aha la hoi ka Ioane mau haumana e hookeai pinepine ai me ka pule, a pela hoi ka ka poe Parisaio; aka hoi, o kau, e ai no, a e inu no?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 I mai la oia ia lakou, E hiki anei ia oukou ke hoolilo i na kanaka o ke keena mare i ka hookeai, i ka manawa e noho pu ai ke kane mare me lakou?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 E hiki mai ana na la e laweia 'ku ai ke kane mare, mai o lakou aku nei, alaila lakou e hookeai ai, ia mau la.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Olelo mai la ia i ka olelonane ia lakou; Aohe kanaka e pinai i ka apana lole hou ma ka lole kahiko, o moku hou auanei ka mea kahiko i ka mea hou, aole hoi e ku ka apana o ka mea hou i ka mea kahiko.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Aohe hoi mea nana e ukuhi i ka waina hou iloko o na huewai ili kahiko, o poha na hue i ka waina hou, a kahe ka waina, a make pu na hue.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Aka, e ukuhiia ka waina hou iloko o na hue hou, a pau pu ua mau mea la i ka malamaia.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Aole mea i inu i ka waina kahiko a makemake koke i ka waina hou; no ka mea, olelo no ia, ua oi ka maikai o ka mea kahiko.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luka 5 >