< Luka 1 >

1 NO ka mea, he nui ka poe i hoao i ka hooponopono i ka mooolelo no na mea i hanaia iwaena o makou,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 E like mo ka hai ana mai ia makou a ka poe ike maka, mai ke kumu mai, ka poe hoalewehana hoi no ka olelo.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Manao iho la au he mea pono no'u, i ko'u huli ikaika ana a maopopo ia mau mea a pau, mai kinohi mai, e palapala hoakaka ia oe, e Teopilo ka mea kaalana,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 I ike oe i ka oiaio o ua mau mea la i aoia'ku ai oe.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 IKE au ia Herode ke alii o Iudea, e noho ana kekahi kahuna, o Zakaria kona inoa, no ka papa o Abia; a o kana wahine, no na kaikamahine ia a Aarona, o Elisabeta kona inoa.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ua pono pu laua imua o ke Akua, e hele hala ole ana ma na kanawai a me na oihana a pau a ka Haku.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Aohe hoi a laua keiki, no ka mea, he pa o Elisabeta; a he nui no hoi ka laua mau makahiki.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Eia kekahi, i kana hana ana i ka oihana kahuna imua o ke Akua, i ka manawa o kona papa,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Mamuli o ka oihana mua a ke kahuna, o kana hana keia, e kuni i ka mea ala i kona hele ana iloko o ka luakini o ka Haku.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 E pule ana ka ahakanaka a pau mawaho, i ka hora i kukuniia'i ka mea ala.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Alaila ikeia aku la ka anela a ka Haku, e ka ana ma ka aoao akau o ke kuahu mea ala.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 A ike aku o Zakaria ia ia, pihoihoi iho la ia, a kau mai la ka makau ia ia.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 I mai la ka anela ia ia, Mai makau oe, e Zakaria, no ka mea, ua loheia kau pule; a e hanau ana kau wahine o Elisabeta i keiki kane nau, a e kapa aku oe i kona inoa o Ioane.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 A o hauoli ana hoi oe me ka olioli, a he nui no hoi ka poe e hauoli i kona hanau ana.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 No ka mea, e nui auanei oia imua o ka Haku; aole ia e inu i ka waina, aole hoi i ka mea awaawa; o piha no hoi ia i ka Uhane Hemolele, mai ka opu mai o kona makuwahine.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 E nui no hoi na mamo a Iseraela ana e hoohuli ai ma ka Haku, ma ko lakou Akua.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 E hele ana hoi ia mamua ona, me ka uhane a me ka mana o Elia, e hoohuli i ka naau o na makua i ka lakou mau keiki, a i ka poe lohe ole mamuli o ka naauao o ka poe pono; e hooponopono ai i kanaka makaukau no ka Haku.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Ninau aku la o Zakaria i ka anela, Mahea la wau e ike ai ia mea? No ka mea, he kanaka kahiko wau, a he nui no hoi na makahiki o ka'u wahine.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Olelo mai la ka anela, i mai la ia ia, Owau no o Gaberiela, ka mea e ku ana imua o ke Akua; a ua hoounaia mai nei au e olelo ia oe, a e hai aku ia oe ia mau mea olioli.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Aia hoi, o paa ana kou leo, aole e hiki ia oe ke olelo, a hiki i ka la e ko ai ia mau mea, no ka mea, aole oe i manaoio mai i ka'u mau olelo, o hookoia auanei ia i ko lakou manawa.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Kakali ae la na kanaka ia Zakaria, haohao iho la i kona loihi ana maloko o ka luakini.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 A puka ia iwaho, aole i hiki ia ia ke olelo mai ia lakou; a ike iho la lakou, ua ike oia i ka mea ikea iloko o ka luakini; no ka mea, kunou oia ia lakou, a ua paa no kona leo.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Eia kekahi, i ka pau ana'e o na la o kana hana, hoi koke no ia i kona hale.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 A, mahope iho o ia mau la, hapai iho la kana wahine, o Elisabeta, a noho mehameha iho la ia i na malama elima, i iho la,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Oia ka ka Haku i hana mai ai no'u ia mau ia ana i manao mai ai e lawe aku i ka mea a'u i hoinoia mai ai iwaena o kanaka.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 A i ke ouo o ka malama, na hoounaia mai o Gaberiela, mai ke Akua mai, i kekahi kulanakauhale i Galilaia, o Nazareta ka inoa,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 I ka wahine puupaa i hoopalauia na kekahi kanaka, o Iosepa ka inoa, no ka ohana a Davida; a o Maria ka inoa o ua wahine puupaa la.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 A komo ka anela io na la, i mai la ia, Aloha oe, e ka mea i aloha nui ia, o ka Haku pu me oe. Pomaikai loa oe iwaena o na wahine.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 A ike aku la, hopohopo iho la oia i kana olelo, a nalu iho la i ke ano o keia aloha ana.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 I mai la ka anela ia ia, Mai makau oe, e Maria; no ka mea, ua loaa ia oe ka lokomaikaiia mai e ke Akua.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Eia hoi, e hapai auanei oe, a e hanau i ke keikikane, a e kapa iho oe i kona inoa, o IESU.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 E nui auanei oia, a e kapaia 'ku, O ke Keiki a ka Mea kiekie loa; a e haawi hoi nona o Iehova ke Akua i ka nohoalii o Davida o kona makuakane.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 E mau loa no hoi kona alii ana maluna o ka ohana a Iakoba; a o kona aupuni aole ia e pau. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Alaila, ninau aku la o Maria i ka anela, Pehea la uanei ia mea? no ka mea, aole au ike i ke kane.
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Olelo mai la ka anela, i mai la ia ia, E kau mai no ka Uhane Hemolele maluna iho ou; a e hoomalu mai ka mana o ka Mea kiekie loa ia oe, no ia mea la hoi, e kapaia ka mea hemolele au e hanau ai, o ke Keiki a ke Akua.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Aia hoi, o Elisabeta o kou hoahanau, ua hapai ae nei i ke keikikane i kona wa luwahine; eia hoi ke ono o ka malama o ka wahine i iia'e he pa.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 No ka mea, aohe mea hiki ole i ke Akua.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 I aku la o Maria, Eia hoi ke kauwa wahine a ka Haku; e like me kau olelo, pela e hanaia mai ai no'u. Alaila, hele aku la ka anela mai ona aku.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Ia mau la, eu ae la o Maria, a hele wikiwiki aku la i ka aina manua, i kekahi kulanakauhale o Iuda;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 A komo aku ia iloko o ka hale o Zakaria, a aloha aku la ia Elisabeta,
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Eia kekahi, i ka wa i lohe ai o Elisabeta i ko Maria aloha, lele iho la ke keiki iloko o kona opu; a hoopihaia o Elisabeta i ka Uhane Hemolele;
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 A olelo mai la oia me ka leo nui, i mai la, Pomaikai loa oe iwaena o na wahine, Pomaikai hoi ka hua o kou opu,
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Nohea mai keia ia u, i hele mai nei ka makuwahine o ko'u Haku io'u nei?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 No ka mea, aia hoi, i ka pae ana mai o kou aloha iloko o ko'u mau pepeiao, lele koke ae nei ke keiki i ka olioli iloko o ko'u opu.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Pomaikai hoi ka wahine i manaoio; e hanaia no na mea i haiia mai ia ia e ka Haku.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Alaila, i aku la o Maria, Ke hoonani aku nei kuu uhane i ka Haku;
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Hauoli no hoi ko'u uhane i ke Akua i ko'u mea e ola'i;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 No ka mea, ua nana aloha mai oia i ka haahaa o kana kauwa wahine, Eia hoi, ma neia hope aku e iia mai au e na hanauna a pau, He pomaikai.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 No ka mea, o ka Mea mana, ua hana mai ia i na mea nani no'u. He hemolele hoi kona inoa.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 E mau ana kona aloha i ka poe makau ia ia, ia hanauna aku ia hanauna aku.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Ua hoike mai oia i ka mana ma kona lima. Ua hoopuehu i ka poe i haaheo i ka manao o ko lakou naau.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Ua kiola iho la oia i na'lii ilalo mai luna mai o ko lakou mau nohoalii; a ua hookiekie ae hoi oia i ka poe haahaa.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Ua hoomaona mai oia i ka pololi i na mea maikai; a ua hookuke hoi oia i ka poe waiwai me ka nele.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Ua kokua mai oia i kana hanai ia Iseraela, me ka hoomanao i ke aloha,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Mamuli o kana olelo na ko kakou poe kupuna, ia Aberahama, a me kona hua a mau loa aku. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Noho pa iho la o Maria me Elisabeta ekolu paha malama, alaila hoi ia i kona hale.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 A hiki ko Elisabeta manawa e hanau ai; hanau iho la oia i ke keikikane.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Lohe iho la na hoalauna, a me na hoahanau ona, i ko ka Haku lokomaikai nui ana ia ia; a olioli pu ae la lakou me ia.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Eia kekahi, i ka walu o ka la hele mai lakou e okipoepoe i ke keiki; kapa ae la lakou ia ia mamuli o ka inoa o kona makuakane, o Zakaria.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Olelo aku la kona makuwahine, i aku la, Aole; aka, e kapaia 'ku no ia o Ioane.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 I mai la lakou ia ia, Aole ou boahanau i kapaia'ku ma keia inoa.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Ninau ae la lakou ma ke kunou ana i kona makuakane i ka inoa ana i makemake ai e kapaia'ku oia.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Noi ae la ia i papa palapala, kakau iho la, i ae la, O Ioane kona inoa. A kahaha iho la ko loko o lakou a pau.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 A wehe koke ia iho la kona waha a me kona elelo, a olelo aku la ia me ka hoolea i ke Akua.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Kau mai la hoi ka makau maluna o ka poe a pau e kokoke mai ana ia lakou. Kukui ae la ka lono o ua mau mea la a puni ka aina manua o Iudea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 A o ka poe a pau i lobe, nalu iho la lakou ma ko lakou mau naau, e i ana iho, Heaha la uanei ke ano o keia keiki? Aia me ia ka lima o ka Haku.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 A o Zakaria kona makuakane, ua piha ia i ka Uhane Hemolele, wanana mai la oia, i mai la,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 E hoomaikaiia ka Haku ke Akua o ka Iseraela; no ka mea, ua ike mai, a ua hoola hoi ia i kona poe kanaka.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Ua kukulu mai nei oia i mea mana e ola'i no kakou, iloko o ka hale o Davida o kana kauwa;
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 E like me kana i hai mai ai ma ka waha o kana mau kaula hemolele mai ke kumu mai o ke ao nei: (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 E pakele ai kakou i ko kakou poe enemi, a i ka lima hoi o ka poe a pau e inaina mai ia kakou;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 E hana lokomaikai ana mai i ko kakou poe kupuna, a me ka hoomanao ana hoi i kana berita hemolele:
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 I ka mea hoohiki ana i hoohiki ai no Aberahama, no ko kakou kupuna,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 E haawi mai oia ia kakou, i ka pakele ana i ka lima o ko kakou poe enemi, e malama wiwo ole aku kakou ia ia,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 Me ka hemolele a me ka pono imua o kona alo, i na la a pau o ke ola ana o kakou.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 A o oe, e ke keiki nei, e kapaia'e oe, He kaula na ka mea kiekie loa; no ka mea, e hele ana oe imua o ka maka o ka Haku, e hoomakaukau i na alanui nona;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 E hoike ana i kona poe kanaka i ke ola, ma ke kala ana iho i ko lakou mau hewa,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 No ka lokomaikai io o ko kakou Akua; no kahi mea i puka mai ai ka malamalama ia kakou mai luna mai,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 E hoomalamalama i ka poe e noho ana i ka pouli, a iloko hoi o ka malu o ka make, a e alakai hoi i ko kakou mau wawae ma ka aoao e maluhia ai.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 A nui ae la ua keiki la, ikaika ae la hoi kona manao; ma na wahi nahele no hoi ia, a hiki i ka la o kona hoikeia i ka Iseraela.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luka 1 >