< Epeso 6 >

1 E NA keiki, e hoolohe i ko oukou mau makua no ka Haku: no ka mea, he pono keia.
Ku’ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku, gama ku na Ubangiji, abin da ya dace ku yi ke nan.
2 E hoomaikai oe i kou makuakane a me ka makuwahine; o ke kauoha mua keia, e pili ana me ka olelo e pomaikai ai:
Doka ta farko wadda aka haɗa da alkawari ita ce, “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,
3 I pomaikai ai oe, i loihi ai hoi kou noho ana ma ka honua.
don ka zauna lafiya, ka kuma yi tsawon rai a duniya.”
4 Oukou boi, e na makua, mai hoonaukiuki aku i na keiki a oukou; aka, e alakai ia lakou ma ka hoopono a me ka hoonaauao a ka Haku.
Ku kuma iyaye, kada ku tsokane’ya’yanku. Ku yi musu reno mai kyau. Ku koyar da su, ku kuma gargaɗe su game da Ubangiji.
5 E na kauwa, e hoolohe oukou i na haku o oukou ma ke kino, me ka makau a me ka weliweli, a me ke kupono o ko oukou naau, e like me ia Kristo:
Ku bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya. Ku nuna musu halin bangirma, kuna kuma yin musu biyayya cikin dukan abu, da zuciya ɗaya kamar ga Kiristi kuke yi.
6 Aole ma ka hooikaika ike maka ia mai, e like me ka poe hoolealea i kanaka; aka, e like me na kauwa a Kristo, e hana ana i ka makemake o ke Akua ma ka naau;
Ku yi aiki sosai, ba don kawai ku gamshe su sa’ad da suke kallonku ba. Da yake ku bayin Kiristi ne, ku aikata nufin Allah da dukan zuciyarku.
7 Me ka naau oluolu e hookauwa ana na ka Haku, aole na kanaka.
Ku yi aikinku da kyakkyawar niyya, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba mutane ba.
8 E ike hoi oukou, a i haua kekahi i ka mea maikai, e ukuia mai oia e ka Haku, o ka mea paa a me ka mea paa ole.
Gama kun san cewa Ubangiji zai ba da lada ga kowa gwargwadon kowane aiki nagarin da ya yi, ko shi bawa ne, ko’yantacce.
9 Oukou hoi, e na haku, pela hoi oukou e hana aku ai ia lakou, aole ka hooweliweli aku; e manao oukou, aia ka lani ka Haku o oukou iho; aole boi ia ia ka nana mai ma ko ke kanaka kino.
Ku kuma masu bayi, dole ku bi da bayinku da kyau. Ku daina ba su tsoro. Ku tuna, ku da su, Maigida ɗaya kuke da shi a sama, kuma ba ya nuna bambanci.
10 Eia hoi, o na hoahanau o'u, i ikaika oukou ma ka Haku, a ma ka ikaika o kona mana.
A ƙarshe, bari ƙarfin ikon Ubangiji yă ba ku ƙarfi.
11 E aahu iho oukou i ke kahiko a pau a ke Akua, i hiki ia oukou ke kupaa imua o na hana maalea a ka diabolo.
Ku yafa dukan kayan yaƙin da Allah yake bayarwa, don ku iya kāre kanku daga dabarun Shaiɗan.
12 No ka mea, aole kakou e hakoko ana me ka mea io a me ka mea koko; aka me na alii, na mea ikaika, na haku o ka pouli o keia ao, a me na uhane ino o ka lewa. (aiōn g165)
Gama ba da mutane da suke nama da jini ne muke yaƙi ba. Muna yaƙi ne da ikoki, da hukumomi, da masu mulkin duhu, da kuma a ikokin da suke cikin a sararin sama. (aiōn g165)
13 No ia hoi, e lawe oukou i ke kahiko a pau a ke Akua, i pono ia oukou ke kupaa, ke hiki mai ka la ino; a pau ae la na mea i ka hanaia, e kupaa oukou.
Saboda haka sai ku yafa dukan kayan yaƙi na Allah, domin sa’ad da ranar mugun nan ta zo, ku iya yin tsayin daka, bayan kuma kuka gama kome, ku dāge.
14 E ku pono hoi oukou, i kakooia ko oukou puhaka i ka oiaio, a pulikiia oukou i ka paleumauma o ka pono:
Saboda haka fa ku dāge, ku sa gaskiya tă zama ɗamararku, adalci yă zama sulkenku,
15 I haweleia hoi ko oukou wawae i ka makaukau no ka euanelio e malu ai.
shirin kai bisharar salama yă zama kamar takalmi a ƙafafunku.
16 Maluna oia mau mea a pau, e lawe hoi i ka aabuapoo o ka manaoio, i mea e hiki ai ia oukou ke kinai iho i na iho wela a pau o ka mea ino.
Ban da waɗannan kuma, ku ɗauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku iya kashe dukan kibiyoyin wutar Mugun nan da ita.
17 E lawe hoi i ka mahiole o ke ola, a me ka pahikaua o ka Uhane, oia no ka olelo a ke Akua:
Ku kuma ɗauki hular kwano na ceto, da takobin Ruhu, wato, Maganar Allah.
18 E pule mau ana i na pule a pau, a me ka nonoi aku ma ka U hane; a no ia mea hoi, e kiai oukou me ka hooikaika mau a me ka pule aku no na haipule a pau;
A koyaushe ku kasance kuna addu’a da roƙo ta wurin ikon Ruhu ba fasawa. A kan wannan manufa ku zauna a faɗake da matuƙar naci, kuna yin wa dukan mutanen Ubangiji addu’a.
19 A ia'u hoi, i haawiia mai ia'u ka olelo e hai aku ai kuu waha me ka makau ole, e hoike aku i ka mea pohihihi o ka euanelio;
Ku kuma yi addu’a domina, don duk sa’ad da na buɗe bakina, in sami kalmomi babu tsoro, don in sanar da asirin bishara,
20 No ia mea, he elele no wau e paa ana i ke kaulahao: i olelo wiwo ole aku au ilaila, e liko me ka'u pono e ololo aku ai.
wadda nake jakadanta cikin sarƙoƙi. Ku yi addu’a don in iya yin shelarta babu tsoro, yadda ya kamata in yi.
21 I ike hoi oukou i ka'u mau mea e noho noi, a me ka'u hana ana, na Tukiko he hoahanau aloha, he lawehana malama pono hoi i ka ka Haku, nana e hoike aku i na mea a pau ia oukou:
Tikikus, ƙaunataccen ɗan’uwa da kuma amintaccen bawa cikin Ubangiji, zai faɗa muku kome, domin ku ma ku san yadda nake, da kuma abin da nake yi.
22 Oia ka'u i hoouna aku ai ia oukou no keia mea, i ike ai oukou i ka wakou, i hooluolu aku ai boi oia i ko oukou naau.
Na aike shi gare ku musamman don wannan, domin ku san yadda muke, yă kuma ƙarfafa ku.
23 I pomaikai na hoahanau, i aloha hoi me ka manaoio, mai ke Akua ka Makua mai, a me ka Haku Iosu Kristo.
’Yan’uwa, salama tare da ƙauna da kuma bangaskiya daga Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi su kasance tare da ku.
24 E alohaia ka poe a pau i aloha io aku i ko kakou Haku ia Iesu Kristo. Amene.
Alheri yă tabbata ga dukan masu ƙaunar Ubangiji Yesu Kiristi da ƙauna marar ƙarewa.

< Epeso 6 >