< II Na Lii 3 >

1 A LILO iho la o Iorama ke keiki a Ahaba i alii maluna o ka Iseraela ma Samaria, i ka makahiki he umi kumamawalu o Iehosapata, ke alii o ka Iuda, a he umikumamalua na makahiki ona i alii ai.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Hana ino aku la ia imua o Iehova, aole nae i like me ka kona makuakane a me ka kona makuwahine; no ka mea, lawe aku la ia i ke kii o Baala, ka mea a kona makuakane i hana'i.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Aka, hoopili aku la ia i na hewa o Ieroboama ke keiki a Nebata, nana i hoolilo ka Iseraela i ka hewa; aole ia i haalele ia mau mea.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 A o Mesa ke alii o ka Moaba, he mea malama holoholona, a hookupu aku la ia no ke alii o ka Iseraela, i hookahi haneri tausani hipakeiki, a i hookahi haneri tausani hipakane me ka hulu.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 A i ka wa i make ai o Ahaba, kipi mai la ke alii o ka Moaba i ke alii o ka Iseraela.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 A hele aku la o Iorama ke alii mai Samaria aku, a helu aku i ka Iseraela a pau.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 Hele aku la ia, a hoouna aku io Iehosapata la ke alii o ka Iuda, i aku la, Ua kipi mai ke alii o ka Moaba ia'u: e hele pu anei oe me au e kaua aku i ka Moaba? I mai la ia, E hele no wau; ua like au me oe, ua like ko'u kanaka me kou kanaka, ua like ko'u mau lio me kou mau lio.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 A ninau mai la ia, Ma ke ala hea kaua e pii aku ai? I aku la ia, Ma ke ala o ka waonahele o Edoma.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 A hele aku la ke alii o ka Iseraela, a me ke alii o ka Iuda, a me ke alii o ka Edoma; a hele poai lakou i ka hele ana i na la ehiku, aohe wai no ka poe kaua, a no na holoholona mahope o lakou.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 I iho la ke alii o ka Iseraela, Auwe! no ka mea, ua hoakoakoa mai o Iehova i keia mau alii ekolu e hoolilo ia lakou iloko o ka lima o ka Moaba!
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 I mai o Iehosapata, Aole anei he kaula a Iehova maanei, i ninau aku ai kakou ia Iehova ma ona la? Olelo aku la kekahi o na kauwa a ke alii o ka Iseraela, i aku la, Eia no o Elisai, ke keiki a Sapata, ka mea i ninini i ka wai maluna o na lima o Elia.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 I mai la o Iehosapata, Ia ia no ka olelo a Iehova, A hele aku la ke alii o ka Iseraela, a me Iehosapata, a me ke alii o ka Edoma, io na la.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Ninau mai la o Elisai i ke alii o ka Iseraela, Heaha ka'u ia oe? e hele oe i na kaula a kou makuakane, a me na kaula a kou makuwahine. I aku la ke alii o ka Iseraela ia ia, Aole, no ka mea, ua hoakoakoa mai o Iehova i keia mau alii ekolu, e hoolilo ia lakou iloko o ka lima o ka Moaba.
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 I mai la o Elisai, Ma ke ola o Iehova o na kaua, imua ona a'u e ku nei, ina i manao ole au ia Iehosapata ke alii o ka Iuda, aole au e nana aku ia oe, aole hoi e ike ia oe.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 E lawe mai i o'u nei i ka mea nana e hookani. A i kana hookani ana, maluna ona ka lima o Iehova.
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 I mai la ia, Ke olelo mai nei o Iehova peneia, E hana i na luawai a paapu keia awawa.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 No ka mea, ke olelo mai nei o Iehova peneia, Aole oukou e ike i ka makani, aole hoi oukou e ike i ka ua; aka, e hoopihaia auanei keia awawa i ka wai i inu ai oukou, a me na bipi a oukou, a me na holoholona a oukou.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 A he mea uuku keia i na maka o Iehova; e haawi no hoi ia i ka Moaba iloko o ko oukou lima.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 A e luku aku oukou i na kulanakauhale a pau i paa i ka pa pohaku, a me na kulanakauhale maikai a pau, a e kua aku oukou i na laau maikai a pau, a e pani aku i na punawai a pau, e luku aku hoi i na kihapai maikai a pau i ka pohaku.
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 A i kakahiaka, i ka manawa i kaumahaia'ku ai ka mohai ai, aia hoi, kahe mai la ka wai mai ka aoao o Edoma mai, a hoopihaia ka aina i ka wai.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 A lohe ka Moaba a pau, ua hele mai na 'lii e kaua me lakou, hoakoakoa ae la lakou i na mea a pau e kaei ana i ke kaei kaua, a keu aku, a ku lakou ma ka mokuna.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Ala ae la lakou i kakahiaka nui, a puka mai ka la maluna o ka wai, a ike aku la ka Moaba i ka wai mai o lakou aku, he ulaula e like me ke koko.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 I ae la lakou, He koko keia; ua lukuia na'lii, ua pepehi kekahi i kekahi; ina kakou i ka waiwai pio, e ka Moaba.
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 A hiki aku lakou i kahi hoomoana o ka Iseraela, ku mai la ka Iseraela, a pepehi mai la i ka Moaba, a hee aku la imua o lakou; a komo aku la lakou iloko, a pepehi aku la i ka Moaba.
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 A wawahi aku la lakou i na kulanakauhale, a hoolei aku la kela kanaka keia kanaka i kona pohaku ma na kihapai maikai a pau a hoopiha iho la; a pani aku la lakou i na punawai a pau, a kua aku la i na laau maikai a pau, a koe aku la na pohaku iloko o Kireharaseta; aka, hoopuni aku la nae na mea maa, a luku aku la ia.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 A ike aku la ke alii o ka Moaba, ua ikaika mai ke kaua ia ia, lawe aku la ia i ehiku haneri kanaka mea pahikaua, a hooikaika e hiki aku i ke alii o ka Edoma, aole nae lakou i hiki.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Alaila lawe aku la ia i kana keiki hiapo, i ka mea nona ke aupuni mahope ona, a kaumaha aku ia ia i mohaikuni maluna o ka papohaku. A ua nui ka inaina i ka Iseraela; a haalele lakou ia ia, a hoi aku la i ka aina.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< II Na Lii 3 >