< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali.
Jesus saiu do templo, e se foi. Então seus discípulos se aproximaram dele para lhe mostrarem os edifícios do complexo do templo.
2 Amma ya amsa masu yace, “kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba.”
Mas Jesus lhes disse: Não vedes tudo isto? Em verdade vos digo, que não será deixada aqui pedra sobre pedra, que não seja derrubada.
3 Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, “me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?” (aiōn g165)
E, depois de se assentar no monte das Oliveiras, os discípulos se aproximaram dele reservadamente, perguntando: Dize-nos, quando serão estas coisas, e que sinal haverá da tua vinda, e do fim da era? (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa yace dasu, “Ku kula kada wani yasa ku kauce.”
E Jesus lhes respondeu: Permanecei atentos, para que ninguém vos engane.
5 Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, “ni ne almasihu,” kuma za su sa da yawa su kauce.
Porque muitos virão em meu nome, dizendo: “Eu sou o Cristo”, e enganarão a muitos.
6 Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna.
E ouvireis de guerras, e de rumores de guerras. Olhai que não vos espanteis; porque é necessário, que [isto] aconteça, mas ainda não é o fim.
7 Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam.
Pois se levantará nação contra nação, e reino contra reino; e haverá fomes, e terremotos em diversos lugares.
8 Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
Mas todas estas coisas são o começo das dores.
9 Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana.
Então vos entregarão para serdes afligidos, e vos matarão; e sereis odiados por todas as nações, por causa do meu nome.
10 Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna.
E muitos tropeçarão na fé; e trairão uns aos outros, e uns aos outros se odiarão.
11 Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
E muitos falsos profetas se levantarão, e enganarão a muitos.
12 Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi.
E, por se multiplicar a injustiça, o amor de muitos se esfriará.
13 Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto.
Mas o que perseverar até o fim, esse será salvo.
14 Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
E este Evangelho do Reino será pregado em todo o mundo, como testemunho a todas as nações, e então virá o fim.
15 Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta),
Portanto, quando virdes que a abominação da desolação, dita pelo profeta Daniel, está no lugar santo, (quem lê, entenda),
16 bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu,
então os que estiveram na Judeia fujam para os montes;
17 Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa,
o que estiver no sobre o telhado não desça para tirar as coisas de sua casa;
18 kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
e o que estiver no campo não volte atrás para tomar a sua capa.
19 Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin!
Mas ai das grávidas e das que amamentarem naqueles dias!
20 Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci.
Orai, porém, para que a vossa fuga não aconteça no inverno, nem no sábado.
21 Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma.
Pois haverá então grande aflição, como nunca houve desde o princípio do mundo até agora, nem jamais haverá.
22 In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
E se aqueles dias não fossem encurtados, ninguém se salvaria; mas por causa dos escolhidos, aqueles dias serão encurtados.
23 Sa'annan idan wani yace maku, duba, “ga Almasihu a nan!” ko, “ga Almasihu a can!” kar ku gaskata.
Então, se alguém vos disser: “Olha o Cristo aqui”, ou “[Olha ele] ali”, não creiais,
24 Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun.
pois se levantarão falsos cristos e falsos profetas; e farão tão grandes sinais e prodígios que, se fosse possível, enganariam até os escolhidos.
25 Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
Eis que eu tenho vos dito com antecedência.
26 Saboda haka, idan suka ce maku, “ga shi a jeji,” kar ku je jejin. Ko, “ga shi a can cikin kuryar daki,” kar ku gaskata.
Portanto, se vos disserem: “Eis que ele está no deserto”, não saiais; “Eis que ele está em um recinto”, não creiais.
27 Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama.
Porque, assim como o relâmpago, que sai do oriente, e aparece até o ocidente, assim também será a vinda do Filho do homem.
28 Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
Onde estiver o cadáver, ali se ajuntarão os abutres.
29 Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
E logo depois da aflição daqueles dias, o sol se escurecerá, a lua não dará o seu brilho, as estrelas cairão do céu, e as forças dos céus se estremecerão.
30 Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Então aparecerá no céu o sinal do Filho do homem. Naquela hora todas as tribos da terra lamentarão, e verão ao Filho do homem, que vem sobre as nuvens do céu, com poder e grande glória.
31 Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
E enviará os seus anjos com grande trombeta, e ajuntarão os seus escolhidos desde os quatro ventos, de uma extremidade à outra dos céus.
32 Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa.
Aprendei a parábola da figueira: “Quando os seus ramos já ficam verdes, e as folhas brotam, sabeis que o verão [está] perto”.
33 Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
Assim também vós, quando virdes todas estas coisas, sabei que já está perto, às portas.
34 Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru.
Em verdade vos digo que esta geração não passará, até que todas estas coisas aconteçam.
35 Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
O céu e a terra passarão, mas minhas palavras de maneira nenhuma passarão.
36 Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
Porém daquele dia e hora, ninguém sabe, nem os anjos do céu, nem o Filho, a não ser meu Pai somente.
37 Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum.
Assim como foram os dias de Noé, assim também será a vinda do Filho do homem.
38 A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin,
Pois, assim como naqueles dias antes do dilúvio comiam, bebiam, casavam, e davam-se em casamento, até o dia em que Noé entrou na arca;
39 ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
e não sabiam, até que veio o dilúvio, e levou todos, assim também será a vinda do Filho do homem.
40 Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya.
Naquela hora dois estarão no campo; um será tomado, e o outro será deixado.
41 Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar.
Duas estarão moendo em um moinho; uma será tomada, e a outra será deixada.
42 Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
Vigiai, pois, porque não sabeis em que dia o vosso Senhor virá.
43 Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba.
Porém sabei isto: se o dono de casa soubesse a que hora da noite o ladrão viria, vigiaria, e não deixaria invadir a sua casa.
44 Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
Portanto também vós estai prontos, porque o Filho do homem virá na hora que não esperais.
45 To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci?
Pois quem é o servo fiel e prudente, ao qual o [seu] senhor pôs sobre os seus trabalhadores, para [lhes] dar alimento no tempo devido?
46 Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo.
Feliz será aquele servo a quem, quando o seu senhor vier, achar fazendo assim.
47 Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
Em verdade vos digo que ele o porá sobre todos os seus bens.
48 Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, “maigida na ya yi jinkiri,”
Porém se aquele servo mau disser em seu coração: “Meu senhor está demorando”,
49 sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya,
e começar a espancar os seus companheiros de serviço, e a comer, e a beber com os beberrões,
50 uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba.
o senhor daquele servo chegará num dia que ele não espera, e numa hora que ele não sabe,
51 Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.
e o despedaçará, e porá sua parte com os hipócritas; ali haverá pranto e ranger de dentes.

< Mattiyu 24 >