< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali.
And Jesus went out of the Temple, and on the way his disciples came to him, pointing out the buildings of the Temple.
2 Amma ya amsa masu yace, “kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba.”
But he, answering, said to them, See you not all these things? truly I say to you that here there will not be one stone resting on another, which will not be pulled down.
3 Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, “me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?” (aiōn g165)
And while he was seated on the Mountain of Olives, the disciples came to him privately, saying, Make clear to us, when will these things be? and what will be the sign of your coming and of the end of the world? (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa yace dasu, “Ku kula kada wani yasa ku kauce.”
And Jesus said to them in answer, Take care that you are not tricked.
5 Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, “ni ne almasihu,” kuma za su sa da yawa su kauce.
For people will come in my name, saying, I am the Christ; and a number will be turned from the true way through them.
6 Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna.
And news will come to you of wars and talk of wars: do not be troubled, for these things have to be; but it is still not the end.
7 Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam.
For nation will be moved against nation, and kingdom against kingdom, and men will be without food, and the earth will be shaking in different places;
8 Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
But all these things are the first of the troubles.
9 Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana.
Then they will be cruel to you, and will put you to death: and you will be hated by all nations because of my name.
10 Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna.
And numbers of people will be turned from the right way, and will give one another up and have hate for one another.
11 Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
And a number of false prophets will come, causing error.
12 Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi.
And because wrongdoing will be increased, the love of most people will become cold.
13 Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto.
But he who goes through to the end will get salvation.
14 Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
And this good news of the kingdom will be given through all the world for a witness to all nations; and then the end will come.
15 Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta),
When, then, you see in the holy place the unclean thing which makes destruction, of which word was given by Daniel the prophet (let this be clear to the reader),
16 bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu,
Then let those who are in Judaea go in flight to the mountains:
17 Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa,
Let not him who is on the house-top go down to take anything out of his house:
18 kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
And let not him who is in the field go back to get his coat.
19 Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin!
But it will be hard for women who are with child and for those with babies at the breast in those days.
20 Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci.
And say a prayer that your flight may not be in the winter, or on a Sabbath.
21 Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma.
Because in those days there will be great sorrow, such as there has not been from the start of the world till now, or ever will be.
22 In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
And if those days had not been made short there would have been no salvation for any, but because of the saints those days will be made short.
23 Sa'annan idan wani yace maku, duba, “ga Almasihu a nan!” ko, “ga Almasihu a can!” kar ku gaskata.
Then if any man says to you, See, here is the Christ, or, Here; do not put faith in him;
24 Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun.
For there will come up false Christs, and false prophets, who will do great signs and wonders; so that if possible even the saints might be tricked.
25 Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
See, I have made it clear to you before it comes about.
26 Saboda haka, idan suka ce maku, “ga shi a jeji,” kar ku je jejin. Ko, “ga shi a can cikin kuryar daki,” kar ku gaskata.
If, then, they say to you, See, he is in the waste land; go not out: See, he is in the inner rooms; put no faith in it.
27 Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama.
Because as in a thunderstorm the bright light coming from the east is seen even in the west; so will be the coming of the Son of man.
28 Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
Wherever the dead body is, there will the eagles come together.
29 Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
But straight away, after the trouble of those days, the sun will be made dark and the moon will not give her light and the stars will come down from heaven and the powers of heaven will be moved:
30 Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma.
And then the sign of the Son of man will be seen in heaven: and then all the nations of the earth will have sorrow, and they will see the Son of man coming on the clouds of heaven with power and great glory.
31 Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
And he will send out his angels with a great sound of a horn, and they will get his saints together from the four winds, from one end of heaven to the other.
32 Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa.
Now take an example from the fig-tree: when her branch has become soft and puts out its leaves, you are certain that the summer is near;
33 Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
Even so, when you see all these things, you may be certain that he is near, even at the doors.
34 Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru.
Truly I say to you, This generation will not come to an end till all these things are complete.
35 Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
Heaven and earth will come to an end, but my words will not come to an end.
36 Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
But of that day and hour no one has knowledge, not even the angels in heaven, or the Son, but the Father only.
37 Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum.
And as were the days of Noah, so will be the coming of the Son of man.
38 A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin,
Because as in those days before the overflowing of the waters, they were feasting and taking wives and getting married, till the day when Noah went into the ark,
39 ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
And they had no care till the waters came and took them all away; so will be the coming of the Son of man.
40 Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya.
Then two men will be in the field; one is taken, and one let go;
41 Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar.
Two women will be crushing grain; one is taken, and one let go.
42 Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
Be watching, then! for you have no knowledge on what day your Lord will come.
43 Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba.
But be certain of this, that if the master of the house had had knowledge of the time when the thief was coming, he would have been watching, and would not have let his house be broken into.
44 Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
Be ready then; for at a time which you have no thought of the Son of man will come.
45 To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci?
Who is the true and wise servant, whom his lord has put over those in his house, to give them their food at the right time?
46 Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo.
A blessing on that servant, who will be doing so when his lord comes.
47 Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
Truly, I say to you, he will put him over all he has.
48 Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, “maigida na ya yi jinkiri,”
But if that evil servant says in his heart, My lord is a long time in coming;
49 sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya,
And is cruel to the other servants, taking his pleasure with those who are overcome with wine;
50 uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba.
The lord of that servant will come in a day when he is not looking for him, and in an hour of which he has no knowledge,
51 Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.
And will have him cut in two, and will give him a part in the fate of the false ones: there will be weeping and cries of sorrow.

< Mattiyu 24 >