< Mattiyu 11 >

1 Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa gargadi, sai ya bar wannan wuri, ya tafi biranensu domin yayi koyorwa, da wa'azi.
And it came to pass, when Jesus ended directing his twelve disciples, he departed thence to teach and to preach in their cities.
2 Da Yahaya mai baftisma ya ji daga kurkuku irin ayyukan da Yesu ke yi, sai ya aika sako ta wurin almajiransa.
And John having heard in the prison the works of the Christ, having sent two of his disciples,
3 Ya ce masa. “Kai ne mai zuwa”? ko mu sa ido ga wani.
said to him, 'Art thou He who is coming, or for another do we look?'
4 Yesu ya amsa ya ce masu, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da ku ka gani da abin da ku ka ji.
And Jesus answering said to them, 'Having gone, declare to John the things that ye hear and see,
5 Makafi suna samun ganin gari, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na jin magana kuma, ana tada matattu, mabukata kuma ana ba su bishara.
blind receive sight, and lame walk, lepers are cleansed, and deaf hear, dead are raised, and poor have good news proclaimed,
6 Kuma mai albarka ne wanda baya tuntube sabili da ni.
and happy is he who may not be stumbled in me.'
7 Bayan wadannan sun tafi, sai Yesu ya fara wa jama'a jawabi game da Yahaya mai baftisma, yana cewa, “Me ake zuwa gani a jeji - ciyawa ce da iska ke busawa?
And as they are going, Jesus began to say to the multitudes concerning John, 'What went ye out to the wilderness to view? — a reed shaken by the wind?
8 Shin menene kuke zuwa gani a jeji - mutum mai sanye da tufafi masu laushi? Hakika, masu sa tufafi masu laushi suna zaune ne a fadar sarakuna.
'But what went ye out to see? — a man clothed in soft garments? lo, those wearing the soft things are in the kings' houses.
9 Amma me ku ke zuwa gani, annabi? Hakika ina fada maku, fiye ma da annabi.
'But what went ye out to see? — a prophet? yes, I say to you, and more than a prophet,
10 Wannan shine wanda aka rubuta game da shi, 'Duba, ina aika manzona, wanda za ya tafi gabanka domin ya shirya maka hanya inda za ka bi'.
for this is he of whom it hath been written, Lo, I do send My messenger before thy face, who shall prepare thy way before thee.
11 Ina gaya maku gaskiya, cikin wadanda mata suka haifa, babu mai girma kamar Yahaya mai baftisma. Amma mafi kankanta a mulkin sama ya fi shi girma.
Verily I say to you, there hath not risen, among those born of women, a greater than John the Baptist, but he who is least in the reign of the heavens is greater than he.
12 Tun daga kwanakin Yahaya mai baftisma zuwa yanzu, mulkin sama yana shan gwagwarmaya, masu husuma kuma su kan kwace shi da karfi.
'And, from the days of John the Baptist till now, the reign of the heavens doth suffer violence, and violent men do take it by force,
13 Gama dukan annabawa da shari'a sun yi annabci har zuwa lokacin Yahaya.
for all the prophets and the law till John did prophesy,
14 kuma in zaku karba, wannan shine Iliya wanda za ya zo.
and if ye are willing to receive [it], he is Elijah who was about to come;
15 Wanda ke da kunnuwan ji, ya ji.
he who is having ears to hear — let him hear.
16 Da me zan kwatanta wannan zamani? Ya na kamar yara masu wasa a kasuwa, sun zauna suna kiran juna
'And to what shall I liken this generation? it is like little children in market-places, sitting and calling to their comrades,
17 suna cewa mun busa maku sarewa baku yi rawa ba, mun yi makoki, baku yi kuka ba.
and saying, We piped unto you, and ye did not dance, we lamented to you, and ye did not smite the breast.
18 Gama Yahaya ya zo, baya cin gurasa ko shan ruwan inabi, sai aka ce, “Yana da aljannu”.
'For John came neither eating nor drinking, and they say, He hath a demon;
19 Dan mutum ya zo yana ci yana sha, sai aka ce, 'Duba, ga mai hadama, mashayi kuma, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!' Amma hikima, ta wurin aikin ta ake tabbatar da ita.
the Son of Man came eating and drinking, and they say, Lo, a man, a glutton, and a wine-drinker, a friend of tax-gatherers and sinners, and wisdom was justified of her children.'
20 Sannan Yesu ya fara tsautawa biranen nan inda ya yi yawancin ayukansa, domin ba su tuba ba.
Then began he to reproach the cities in which were done most of his mighty works, because they did not reform.
21 “Kaiton ki Korasinu, kaiton ki Batsaida! In da an yi irin ayuka masu ban mamaki a Taya da Sidon! Yadda aka yi a cikinku, da tuni sun tuba suna sanye da tsumma da yafa toka.
'Woe to thee, Chorazin! woe to thee, Bethsaida! because, if in Tyre and Sidon had been done the mighty works that were done in you, long ago in sackcloth and ashes they had reformed;
22 Amma zai zama da sauki a kan Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku.
but I say to you, to Tyre and Sidon it shall be more tolerable in a day of judgment than for you.
23 Ke kafarnahum, kina tsammani za a daukaka ki har zuwa sama? A'a za a saukar da ke kasa zuwa hades. Gama in da an yi irin al'ajiban da aka yi a cikin ki a Sodom, da tana nan har yanzu. (Hadēs g86)
'And thou, Capernaum, which unto the heaven wast exalted, unto hades shalt be brought down, because if in Sodom had been done the mighty works that were done in thee, it had remained unto this day; (Hadēs g86)
24 Amma ina ce maku, za a saukaka wa Sodom a ranar shari'a fiye da ku.”
but I say to you, to the land of Sodom it shall be more tolerable in a day of judgment than to thee.'
25 A wannan lokaci Yesu ya ce, “Ina yabon ka, ya Uba, Ubangijin sama da kasa, domin ka boye wa masu hikima da fahimta wadannan abubuwa, ka bayyana wa marasa sani, kamar kananan yara.
At that time Jesus answering said, 'I do confess to Thee, Father, Lord of the heavens and of the earth, that thou didst hide these things from wise and understanding ones, and didst reveal them to babes.
26 I, ya Uba gama wannan shine ya yi daidai a gare ka.
Yes, Father, because so it was good pleasure before Thee.
27 An mallaka mani dukan abu daga wurin Ubana. Sannan babu wanda ya san Dan, sai Uban, babu kuma wanda ya san Uban, sai Dan, da duk wanda ya so ya bayyana masa.
'All things were delivered to me by my Father, and none doth know the Son, except the Father, nor doth any know the Father, except the Son, and he to whom the Son may wish to reveal [Him].
28 Ku zo gare ni, dukanku masu wahala da fama da nauyin kaya, ni kuma zan ba ku hutawa.
'Come unto me, all ye labouring and burdened ones, and I will give you rest,
29 Ku dauki karkiya ta ku koya daga gare ni, gama ni mai tawali'u ne da saukin hali a zuciya, sannan zaku sami hutawa ga rayukanku.
take up my yoke upon you, and learn from me, because I am meek and humble in heart, and ye shall find rest to your souls,
30 Gama karkiyata mai sauki ce, kaya na kuma ba shi da nauyi.”
for my yoke [is] easy, and my burden is light.'

< Mattiyu 11 >