< Mattiyu 10 >

1 Yesu ya kira almajiransa goma sha biyu, ya kuma ba su ikon fitar da kazaman ruhohi, su warkar da kowacce irin cuta da rashin lafiya.
Jesus called his twelve disciples together and gave them power to throw out evil spirits, and to heal all kinds of diseases and sicknesses.
2 To yanzu ga sunayen manzanin nan goma sha biyu. Na farkon shine, Saminu, wanda ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, da Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya;
These are the names of the twelve apostles: first, Simon, (also called Peter), Andrew his brother, James the son of Zebedee, John his brother,
3 Filibus, da Bartalamawus, da Toma da Matiyu mai karbar haraji da Yakubu dan Halfa, da Taddawus;
Philip, Bartholomew, Thomas, Matthew the tax-collector, James the son of Alphaeus, Thaddeus,
4 Saminu Bakairawane, da kuma Yahuza Iskariyoti wanda ya bashe shi.
Simon the revolutionary, and Judas Iscariot, who betrayed Jesus.
5 Sha biyun nan su ne Yesu ya aika, ya yi masu umarni ya ce, ''Kada ku shiga wajen al'ummai, ko kuma kowane garin Samariyawa.
These Twelve Jesus sent out, telling them, “Don't go to the foreigners, or to any Samaritan city.
6 Sai dai ku je wurin batattun tumaki na gidan Isra'ila.
You are to go to the lost sheep of the house of Israel.
7 Sa'adda kuna tafiya, kuna wa'azi, kuna cewa, 'Mulkin Sama ya kusato'.
Wherever you go, tell the people, ‘The kingdom of heaven is near.’
8 Ku warkar da marasa lafiya, ku tada matattu, ku tsarkake kutare, ku kuma fitar da aljanu. Kyauta kuka samu ku ma ku bayar kyauta.
Heal those who are sick. Resurrect the dead. Cure the lepers. Drive out demons. You received freely, so give freely!
9 Kada ku rike zinariya, ko azurfa, ko tagulla a jakarku.
Don't carry any gold, silver, or copper coins in your pockets,
10 Kada kuma ku dauki zabira a tafiyarku, ko taguwa biyu, ko takalma, ko sanda, don ma'aikaci ya cancanci abincin sa.
or a bag for your journey, or two cloaks, or sandals, or a walking stick, for a worker deserves to be supported.
11 Kowanne birni, ko kauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a cikinsa, ku kuma zauna a wurin har lokacin da za ku tashi.
Wherever you go, whatever town or village, ask for someone who lives according to good principles, and remain there until you leave.
12 In za ku shiga gida ku ce, salama a gareku.
When you enter the house, give it your blessing.
13 Idan gidan akwai dan salama, salamarku za ta ta tabbata a gare shi. Idan kuwa babu, salamarku za ta komo maku.
If the home deserves it, let your peace rest on it, but if it doesn't deserve it, let your peace return to you.
14 Ga wadanda su ka ki karbar ku ko sauraron ku, idan za ku fita garin ko gidan, sai ku karkade kurar kafafunku.
If someone doesn't welcome you, and refuses to listen to what you have to say, then leave that house or that town, shaking its dust off your feet as you go.
15 Hakika, ina gaya maku, a ranar shari'a za a fi rangwanta wa kasar Saduma da ta Gwamrata a kan wannan birni.
I tell you the truth, it will be better for Sodom and Gomorrah at the Day of Judgment than for that town!
16 ''Duba, na aike ku kamar tumaki a tsakiyar kyarketai, don haka sai ku zama masu wayo kamar macizai, da kuma marasa barna kamar kurciyoyi.
Look, I'm sending you out like sheep among wolves. So be as wise as serpents and harmless as doves.
17 Ku yi hankali da mutane, don za su kai ku gaban majalisa, su kuma yi maku bulala a majami'unsu.
Watch out for those who will hand you over to be tried by town councils and will whip you in their synagogues.
18 Za su kuma kai ku gaban mahukunta da sarakuna saboda ni, domin ku bada shaida a gabansu, da kuma gaban al'ummai.
You will be dragged before governors and kings because of me, to witness to them and to the foreigners.
19 Idan har sun bada ku, kada ku damu da yadda za ku yi magana, ko kuwa abin da za ku fada, domin za a ba ku abin da za ku fada a lokacin.
But when they put you on trial, don't worry about how you should speak or what you should say, because you'll be told what to say at the right time.
20 Domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhun Ubanku ne yake magana ta bakinku.
For it isn't you who will speak but the spirit of the Father will speak through you.
21 Dan'uwa zai ba da dan'uwansa a kashe shi, uba kuwa dansa. 'Ya'ya kuma za su tayarwa iyayensu, har su sa a kashe su.
Brother will betray brother and have him killed, and a father will do the same to his child. Children will rebel against their parents, and have them put to death.
22 Kowa kuma zai ki ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har karshe, zai tsira.
Everyone will hate you because you follow me, but those who endure until the end will be saved.
23 In sun tsananta maku a wannan gari, ku gudu zuwa na gaba. Hakika ina gaya maku, kafin ku gama zazzaga dukan garuruwan Isra'ila, Dan Mutum zai zo.
When you're persecuted in one town, run away to the next. I'm telling the truth: you won't finish going to the towns of Israel before the Son of man comes.
24 Almajiri ba ya fin malaminsa, bawa kuma ba yafin ubangijinsa.
Disciples are not more important than their teacher; servants are not more important than their master.
25 Dai dai ne almajiri ya zama kamar malaminsa, bawa kuma kamar ubangijinsa. In har sun kira mai gida Ba'alzabuba, za su kuma bata mutanen gidansa!
Disciples should be satisfied to become like their teacher, and servants like their master. If the head of the house has been called the head demon Beelzebub, then the members of his household will be demonized even more!
26 Don haka kada kuji tsoron su, domin ba abin da yake boye da ba za a bayyana ba.
So don't be frightened of them, for there's nothing covered that won't be exposed, and nothing hidden that won't be made known.
27 Abin da nake fada maku a asirce, ku fada a sarari. Abin da kuma kuka ji a cikin rada, ku yi shelarsa daga kan soraye.
What I tell you here in the dark, declare when it's light, and what you hear whispered in your ear, shout from the rooftops.
28 Kada ku ji tsoron masu kisan jikin mutum, amma ba sa iya kashe rai. Sai dai ku ji tsoron wannan da yake da ikon kashe jiki ya kuma jefa rai cikin jahannama. (Geenna g1067)
Don't be afraid of those who can kill you physically, but can't kill you spiritually. Instead, be afraid of the one who can destroy you physically and spiritually in the fires of destruction. (Geenna g1067)
29 Ba 'yan tsuntsaye biyu ake sayarwa akan kobo ba? Ba ko daya a cikin su da zai fadi kasa ba tare da yardar Ubanku ba.
Aren't two sparrows sold for just one penny? But not a single one of them falls to the ground without your Father knowing about it.
30 Ai, ko da gashin kan ku ma duk a kidaye yake.
Even the hairs on your head have all been counted.
31 Kada ku ji tsoro. Gama darajarku ta fi ta tsuntsaye masu yawa.
So don't worry—you're worth more than many sparrows!
32 ''Saboda haka duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, ni ma zan yi shaidar sa a gaban Ubana wanda ya ke cikin Sama.
Anyone who publicly declares their commitment to me, I will also declare my commitment to them before my Father in heaven.
33 Amma duk wanda ya yi musun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi musun sanin sa a gaban Ubana da yake cikin Sama.''
But anyone who publicly denies me, I will also deny before my Father in heaven.
34 ''Kada ku zaci na zo ne in kawo salama a duniya. Ban zo domin in kawo salama ba, sai dai takobi.
Don't think I've come to bring peace on earth. I haven't come to bring peace, but a sword.
35 Domin na zo ne in hada mutum da ubansa gaba, 'ya da uwatarta, mata da kuma surukarta.
I've come ‘to turn a man against his father, a daughter against her mother, and a daughter-in-law against her mother-in-law.
36 Zai zama na kuma magabtan mutum su ne mutanen gidansa.
Your enemies will be those of your own family!’
37 Dukan wanda ya fi son mahaifinsa ko mahaifayarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. Wanda kuma ya fi son dansa ko 'yarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba.
If you love your father or mother more than me you don't deserve to be mine, and if you love your son or daughter more than me you don't deserve to be mine.
38 Wanda kuma bai dauki gicciyensa ya biyo ni ba, bai cancanci zama nawa ba.
If you don't pick up your cross and follow me you don't deserve to be mine.
39 Dukan mai son ya ceci ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, yana ceton sa ne.
If you try to save your life, you will lose it, but if you lose your life because of me you will save it.
40 ''Wanda ya marabce ku, ya marabce ni ke nan.
Those who welcome you welcome me, and those who welcome me welcome the one that sent me.
41 Wanda ya marabce ni kuwa, ya marabci wanda ya aiko ni. Wanda ya marabci annabi domin shi annabi ne, zai karbi lada kamar na annabi. Wanda kuma ya marabci mai adalci saboda shi mai adalci ne, zai sami lada kamar na mai adalci.
Those who welcome a prophet because that's what they are will receive the same reward as a prophet. Those who welcome someone who does right will receive the same reward as someone who does right.
42 Kowa ya ba daya daga cikin 'yan kananan nan, ko da kofin ruwan sanyi ya sha, domin shi almajirina ne, hakika, Ina gaya maku, ba zai rasa ladarsa ba.''
I tell you the truth, those who give a drink of cool water to the least important of my disciples will definitely not miss out on their reward.”

< Mattiyu 10 >