< Markus 1 >

1 Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
The beginning of the Good News of Yeshua the Messiah, the Son of God.
2 kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
As it is written in Isaiah the prophet, "Look, I send my messenger ahead of you, who will prepare your way before you.
3 Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
The voice of one crying in the wilderness, 'Prepare the way of the Lord. Make his roads straight.'"
4 Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
John came immersing in the wilderness and proclaiming the immersion of repentance for forgiveness of sins.
5 Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
And all the country of Judea went out to him and all those from Jerusalem, and they were immersed by him in the Jordan river, confessing their sins.
6 Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
And John was clothed with camel's hair and a leather belt around his waist. He ate locusts and wild honey.
7 Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
And he preached, saying, "After me comes he who is mightier than I, the strap of whose sandals I am not worthy to stoop down and loosen.
8 Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
I immersed you in water, but he will immerse you in the Ruach ha-Kodesh."
9 Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
And it happened in those days, that Yeshua came from Natzeret of Galil, and was immersed by John in the Jordan.
10 Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
Immediately coming up from the water, he saw the heavens parting, and the Ruach descending on him like a dove.
11 Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
And a voice came out of the sky, "You are my beloved Son, with you I am well pleased."
12 Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
And immediately the Ruach drove him out into the wilderness.
13 Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
And he was in the wilderness forty days tempted by Satan. He was with the wild animals; and the angels were serving him.
14 Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
Now after John was taken into custody, Yeshua came into Galil, proclaiming the Good News of God,
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
and saying, "The time is fulfilled, and the Kingdom of God is near. Repent, and believe in the Good News."
16 Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
And passing along by the Lake of Galil, he saw Shim'on and Andrew the brother of Shim'on casting a net into the lake, for they were fishermen.
17 Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
And Yeshua said to them, "Come, follow me, and I will make you into fishers of people."
18 Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
And immediately they left the nets, and followed him.
19 Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
And going on a little further, he saw Jacob the son of Zavdai, and John, his brother, who were also in the boat mending the nets.
20 Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
And immediately he called them, and they left their father, Zavdai, in the boat with the hired servants, and went after him.
21 Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
And they went into Kfar-Nahum, and immediately on the Sabbath day he entered into the synagogue and taught.
22 Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
And they were astonished at his teaching, for he taught them as having authority, and not as the scribes.
23 A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
And just then there was in their synagogue a man with an unclean spirit, and he shouted,
24 Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
saying, "What do we have to do with you, Yeshua of Natzeret? Have you come to destroy us? I know you who you are: the Holy One of God."
25 Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
And Yeshua rebuked him, saying, "Be quiet, and come out of him."
26 Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
And the unclean spirit, convulsing him and crying with a loud voice, came out of him.
27 Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
And they were all amazed, so that they questioned among themselves, saying, "What is this? A new teaching? For with authority he commands even the unclean spirits, and they obey him."
28 Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
And at once the news of him went out everywhere into all the region of Galil and its surrounding area.
29 Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
And immediately, when they had come out of the synagogue, they came into the house of Shim'on and Andrew, with Jacob and John.
30 Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
Now Shim'on's mother-in-law was sick in bed with a fever, and immediately they told him about her.
31 Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
And he came and took her by the hand, and raised her up. The fever left her, and she served them.
32 Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
At evening, when the sun had set, they brought to him all who were sick, and those who were possessed by demons.
33 Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
And all the city was gathered together at the door.
34 ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
And he healed many who were sick with various diseases, and cast out many demons. He did not allow the demons to speak, because they knew him.
35 Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
And early in the morning, while it was still dark, he rose up and went out, and departed into a deserted place, and prayed there.
36 Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
And Shim'on and those who were with him followed after him;
37 Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
and they found him, and told him, "Everyone is looking for you."
38 Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
And he said to them, "Let us go somewhere else into the next towns, that I may preach there also, because I came out for this reason."
39 Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
And he went into their synagogues throughout all Galil, preaching and casting out demons.
40 Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
And a leper came to him, begging him, and knelt down and said to him, "Lord, if you want to, you can make me clean."
41 Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
And being moved with compassion, he stretched out his hand, and touched him, and said to him, "I am willing. Be cleansed."
42 Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
And immediately the leprosy departed from him, and he was made clean.
43 Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
And he strictly warned him, and immediately sent him out,
44 Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
and said to him, "See you say nothing to anyone, but go show yourself to the cohen, and offer for your cleansing the things which Moses commanded, for a testimony to them."
45 Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.
But he went out, and began to proclaim it freely, and to spread about the matter, so that Yeshua could no more openly enter into a city, but was outside in desert places: and they came to him from everywhere.

< Markus 1 >