< Luka 8 >

1 Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
In zgodí se po tem, in on je hodil po mestih in vaséh, učeč in oznanjujoč evangelj o kraljestvu Božjem; in dvanajsteri ž njim,
2 mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
In nektere žene, ktere so uzdravljene bile od duhov hudobnih in od bolezni, Marija, ki se imenuje Magdalena, iz ktere je bilo sedem hudičev izšlo,
3 da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
Joana žena Huza pristavnika Herodovega, in Suzana, in drugih veliko, ktere so mu služile z imenjem svojim.
4 Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
Ko se je pa veliko ljudstva sešlo, in tistih, kteri so iz mest prihajali k njemu, pové jim v priliki:
5 “Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
Izšel je sejalec sejat seme svoje; in ko je sejal, eno je padlo poleg ceste, in pogazilo se je, in tice nebeške so ga pozobale.
6 Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
In drugo je padlo na skalo, in ko je pognalo, usahnilo je, ker ni imelo vlage.
7 Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
In drugo je padlo sredi trnja, in trnje je zrastlo, in udušilo ga je.
8 Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
In drugo je padlo na dobro zemljo, in ko je pognalo, doneslo je stoteri sad. Ko je to pravil, klical je: Kdor ima ušesa, da sliši, naj sliši!
9 Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
Vpraševali pa so ga učenci njegovi, govoreč: Kakošna bi bila ta prilika?
10 ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
On pa reče: Vam je dano, da spoznate skrivnosti kraljestva Božjega; drugim pa v prilikah, da gledajo in ne vidijo, ter slišijo in ne umejo.
11 To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
Ta prilika pa je: Seme je beseda Božja:
12 Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
A kteri so poleg ceste posejani, ti so, kteri slišijo: ali potem pride hudič in vzeme besedo iz srca njih, da ne bi verovali in zveličali se.
13 Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
A kteri so na skalo posejani, ti, kteri besedo, ko so jo sklišali, z veseljem sprejemajo; in ti korenine nimajo, kteri nekaj časa verujejo, a v čas izkušnjave odpadejo.
14 Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
Kar je pa v trnje padlo, to so ti, kteri slišijo: ali ker za skrbmí in bogastvom in slastmi življenja hodijo, udušé se, in ne donašajo sadú.
15 Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
Kar je pa na dobro zemljo padlo, to so ti, kteri v dobrem in blagem srcu varujejo besedo, ktero so slišali, in donašajo sad v trpljenji.
16 Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
Nikdor pa sveče, ko jo prižgè, ne skrije pod mernik, ali dene pod posteljo; nego postavi jo na svečnik, da ti, kteri vhajajo, vidijo luč.
17 Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
Kajti nič ni prikritega, kar se ne bo razodelo; tudi skrivnega ne, kar se ne bo zvedelo in na svetlo prišlo.
18 Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
Glejte torej, kako boste poslušali: kajti kdor imá, dalo mu se bo; a kdor nima, odvzelo mu se bo tudi to, kar misli, da ima.
19 Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
Pridejo pa k njemu mati njegova in bratje njegovi; ali za voljo ljudstva niso mogli priti do njega.
20 Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
In sporočé mu, govoreč: Mati tvoja in bratje tvoji stojé zunej, in radi bi te videli.
21 Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
On pa odgovarjajoč, reče jim: Mati moja in bratje moji so ti, kteri besedo Božjo poslušajo in delajo po njej.
22 Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
In zgodí se en dan, in on stopi v ladjo in učenci njegovi; in reče jim: Prepeljimo se na oni kraj jezera! In odpeljejo se.
23 Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
A ko so se peljali, zaspí. Kar snide vihar na jezero, in potapljali so se, in bili so v nevarnosti.
24 Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
In pristopivši, zbudé ga, govoreč: Učenik! učenik! pogibamo! A on vstavši, zapretí vetru in valovju; in umirita se, in nastala je tihota.
25 Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
In reče jim: Kje je vera vaša? A oni so se uplašili, in začudijo se, govoreč eden drugemu: Kdo neki je ta, da tudi vetrovom zapoveduje in vodi, in poslušajo ga?
26 Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
In preplavijo se v zemljo Gadarensko, ktera je Galileji nasproti.
27 Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
Ko pa izide na zemljo, sreča ga en človek iz mesta, kteri je imel hudiča uže dolgo časa, in v obleko se ni oblačil, in v hiši ni prebival, nego v grobih.
28 Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
A ko ugleda Jezusa, zakričí in pade pred-nj, in z močnim glasom reče: Kaj imaš z menoj, Jezus, sin Boga najvišega: Prosim te, nikar mene muči!
29 Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
Ukazal je bil namreč duhu nečistemu, naj izide iz človeka: kajti uže dolgo časa ga je bil metal, in vezali so ga z verigami in vezmí, ter so ga varovali; ali potrgal je vezí, in gonil ga je hudič po puščavah.
30 Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
Vpraša pa ga Jezus, govoreč: Kako ti je ime? On pa reče: Množica; kajti obsedlo ga je bilo mnogo hudičev.
31 Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
In prosili so ga, naj jim ne zapové iti v brezno. (Abyssos g12)
32 Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
Bila je pa tam velika čreda svinj, ktere so se pasle na gori; in prosili so ga, naj jim dovoli, da vnidejo va-nje. In dovoli jim.
33 Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
In hudiči izidejo iz človeka in vnidejo v svinje; in zakadí se čreda z brega v jezero, in potonejo.
34 Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
Videvši pa pastirji, kar se je zgodilo, pobegnejo, ter odidejo in sporočé po mestu in po vaséh.
35 Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
Ter izidejo gledat, kaj se je zgodilo; in pridejo k Jezusu, in najdejo človeka, iz kterega so bili hudiči izšli, da je oblečen in pameten, in sedí pri nogah Jezusovih; in uplašijo se.
36 Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
Sporočé pa jim tudi ti, kteri so bili videli, kako je obsedenec ozdravel.
37 Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
In zaprosi ga vsa množica iz okolice Gadarenske, naj odide od njih; kajti strah velik jih je preletal. A on stopi v ladjo in se vrne.
38 Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
Prosil pa ga je mož, iz kterega so bili izšli hudiči, da bi bil ž njim; ali Jezus ga odpravi, govoreč:
39 “Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
Vrni se na dom svoj, in pripoveduj, kaj ti je storil Bog. Pa odide, po vsem mestu oznanjujoč, kaj mu je storil Jezus.
40 Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
Zgodí se pa, ko se vrne Jezus, sprejme ga ljudstvo; kajti vsi so ga pričakovali.
41 Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
In glej, pa pride mož, kteremu je bilo ime Jair, (in ta je bil starešina v shajališči, ) in pade Jezusu pred noge, in prosil ga je, naj vnide v hišo njegovo;
42 saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
Kajti imel je hčer edinico pri dvanajstih letih, in ta je umirala. A ko je šel, stiskalo ga je ljudstvo.
43 Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
In žena, ktera je imela krvotok uže dvanajst let, in je bila vse imenje svoje potrošila na zdravnike, ktere ni mogel nobeden uzdraviti.
44 Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
Pristopi od zadi in se dotakne robú obleke njegove; in precej se je ustavil vir krví njene.
45 Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
Pa reče Jezus: Kdo se me je dotaknil? Ko so se pa vsi odgovarjali, reče Peter in kteri so bili ž njim; Učenik, ljudstvo te gnjete in stiska, pa praviš: Kdo se me je dotaknil?
46 Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
Jezus pa reče: Nekdo se me je dotaknil; kajti jaz sem očutil, da je odšla moč od mene.
47 Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
Videč pa žena, da se ni prikrila, pristopi drhtajoč, in pade pred-nj, in pové mu pred vsem ljudstvom, za kaj se ga je dotaknila, in kako je ozdravela precej.
48 Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
On jej pa reče: Zaupaj, hčer! vera tvoja ti je pomogla; pojdi v miru.
49 Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
Ko je še govoril, pride nekdo od starešine shajališčnega, govoreč mu: Umrla je hčer tvoja; ne trudi učenika.
50 Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
Slišavši pa to Jezus, odgovorí mu, govoreč: Ne boj se! le veruj, in ozdravela bo.
51 Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
Ko je pa prišel v hišo, ni dal nikomur vniti, razen Petru in Jakobu in Janezu, in očetu in materi deklice.
52 Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
Vsi pa so jokali, in tarnali po njej. On pa reče: Ne jokajte! ni umrla, nego spí.
53 Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
In posmehovali so mu se, vedoč, da je umrla.
54 Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
On pa izgnavši vse, in prijemši jo za roko, zakliče, govoreč: Deklica, vstani!
55 Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
In vrne se duh nje, in vstala je precej; in ukaže jim, naj jej dadó jesti.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.
In zavzemeta se roditelja njena; a on jima naročí, naj nikomur ne povesta, kar se je zgodilo.

< Luka 8 >