< Luka 8 >

1 Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
После тога иђаше Он по градовима и по селима учећи и проповедајући јеванђеље о царству Божијем, и дванаесторица с Њим.
2 mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
И неке жене које беху исцељене од злих духова и болести: Марија, која се зваше Магдалина, из које седам ђавола изиђе,
3 da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
И Јована, жена Хузе пристава Иродовог, и Сусана, и друге многе које служаху Њему имањем својим.
4 Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
А кад се сабра народа много, и из свих градова долажаху к Њему, каза у причи:
5 “Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
Изиђе сејач да сеје семе своје; и кад сејаше, једно паде крај пута, и погази се, и птице небеске позобаше га,
6 Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
А друго паде на камен, и изникавши осуши се, јер немаше влаге.
7 Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
И друго паде у трње, и узрасте трње, и удави га.
8 Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
А друго паде на земљу добру, и изникавши донесе род сто пута онолико. Говорећи ово повика: Ко има уши да чује нека чује.
9 Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
А ученици Његови питаху Га говорећи: Шта значи прича ова?
10 ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
А Он рече: Вама је дано да знате тајне царства Божијег; а осталима у причама, да гледајући не виде, и чујући не разумеју.
11 To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
А прича ова значи: Семе је реч Божија.
12 Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
А које је крај пута то су они који слушају, али потом долази ђаво, и узима реч из срца њиховог, да не верују и да се не спасу.
13 Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
А које је на камену то су они који кад чују с радости примају реч; и ови корена немају који за неко време верују, а кад дође време кушања отпадну.
14 Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
А које у трње паде, то су они који слушају, и отишавши, од бриге и богатства и сласти овог живота загуше се, и род не сазри.
15 Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
А које је на доброј земљи то су они који реч слушају, и у добром и чистом срцу држе, и род доносе у трпљењу. Ово говорећи повика: Ко има уши да чује нека чује.
16 Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
Нико, пак, свеће не поклапа судом кад је запали, нити меће под одар, него је метне на свећњак да виде светлост који улазе.
17 Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
Јер нема ништа тајно што неће бити јавно, ни сакривено што се неће дознати и на видело изићи.
18 Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
Гледајте, дакле, како слушате; јер ко има, даће му се, а ко нема, узеће се од њега и оно што мисли да има.
19 Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
Дођоше пак к Њему мати и браћа Његова, и не могаху од народа да говоре с Њим.
20 Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
И јавише Му говорећи: Мати Твоја и браћа Твоја стоје напољу, хоће да Те виде.
21 Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
А Он одговарајући рече им: Мати моја и браћа моја они су који слушају реч Божију и извршују је.
22 Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
И догоди се у један дан Он уђе с ученицима својим у лађу, и рече им: Да пређемо на оне стране језера. И пођоше.
23 Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
А кад иђаху они Он заспа. И подиже се олуја на језеру, и топљаху се, и беху у великој невољи.
24 Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
И приступивши пробудише Га говорећи: Учитељу! Учитељу! Изгибосмо. А Он устаде, и запрети ветру и валовима; и престадоше и поста тишина.
25 Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
А њима рече: Где је вера ваша? А они се поплашише, и чуђаху се говорећи један другом: Ко је Овај што и ветровима и води заповеда, и слушају Га?
26 Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
И дођоше у околину гадаринску која је према Галилеји.
27 Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
А кад изиђе Он на земљу, срете Га један човек из града у коме беху ђаволи од много година, и у хаљине не облачаше се, и не живљаше у кући, него у гробовима.
28 Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
А кад виде Исуса, повика и припаде к Њему и рече здраво: Шта је теби до мене, Исусе, Сине Бога Највишег? Молим Те, не мучи ме.
29 Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
Јер Исус заповеди духу нечистом да изиђе из човека: јер га мучаше одавно, и метаху га у вериге и у пута да га чувају, и искида свезе, и тераше га ђаво по пустињи.
30 Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
А Исус га запита говорећи: Како ти је име? А он рече: Легеон; јер многи ђаволи беху ушли у њ.
31 Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
И мољаху Га да им не заповеди да иду у бездан. (Abyssos g12)
32 Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
А онде пасаше по гори велико крдо свиња, и мољаху Га да им допусти да у њих уђу. И допусти им.
33 Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
Тада изиђоше ђаволи из човека и уђоше у свиње; и навали крдо с брега у језеро, и утопи се.
34 Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
А кад видеше свињари шта би, побегоше и јавише у граду и по селима.
35 Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
И изиђоше људи да виде шта је било, и дођоше к Исусу, и нађоше човека из кога ђаволи беху изишли, а он седи обучен и паметан код ногу Исусових; и уплашише се.
36 Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
А они што су видели казаше им како се исцели бесни.
37 Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
И моли Га сав народ из околине гадаринске да иде од њих; јер се беху врло уплашили. А Он уђе у лађу и отиде натраг.
38 Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
Човек, пак, из кога изиђоше ђаволи мољаше да би с Њим био; али га Исус отпусти говорећи:
39 “Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
Врати се кући својој, и казуј шта ти учини Бог. И отиде проповедајући по свему граду шта му Исус учини.
40 Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
А кад се врати Исус, срете Га народ, јер Га сви очекиваху.
41 Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
И гле, дође човек по имену Јаир, који беше старешина у зборници, и паде пред ноге Исусове, и мољаше Га да уђе у кућу његову;
42 saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
Јер у њега беше јединица кћи од дванаест година, и она умираше. А кад иђаше Исус, туркаше Га народ.
43 Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
И беше једна болесна жена од течења крви дванаест година, која је све своје имање потрошила на лекаре и ниједан је није могао излечити,
44 Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
И приступивши састраг дотаче се скута од хаљине Његове, и одмах стаде течење крви њене.
45 Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
И рече Исус: Ко је то што се дотаче мене? А кад се сви одговараху, рече Петар и који беху с њим: Учитељу! Народ Те опколио и турка Те, а Ти кажеш: Ко је то што се дотаче мене?
46 Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
А Исус рече: Неко се дотаче мене; јер ја осетих силу која изиђе из мене.
47 Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
А кад виде жена да се није сакрила, приступи дрхћући, и паде пред Њим, и каза Му пред свим народом зашто Га се дотаче и како одмах оздрави.
48 Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
А Он јој рече: Не бој се, кћери! Вера твоја поможе ти; иди с миром.
49 Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
Док Он још говораше, дође неко од куће старешине зборничког говорећи му: Умре кћи твоја, не труди учитеља.
50 Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
А кад чу Исус, одговори му говорећи: Не бој се, само веруј, и оживеће.
51 Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
А кад дође у кућу, не даде ниједноме ући осим Петра и Јована и Јакова, и девојчиног оца и матере.
52 Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
А сви плакаху и јаукаху за њом; а Он рече: Не плачите, није умрла него спава.
53 Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
И подсмеваху Му се знајући да је умрла.
54 Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
А Он изагнавши све узе је за руку, и зовну говорећи: Девојко! Устани!
55 Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
И поврати се дух њен, и устаде одмах; и заповеди да јој дају нека једе.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.
И дивише се родитељи њени. А Он им заповеди да никоме не казују шта је било.

< Luka 8 >