< Luka 7 >

1 Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
Ko je torej končal vse svoje govore pred občinstvom ljudi, je vstopil v Kafarnáum.
2 Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
Neki služabnik stotnika, ki mu je bil dragocen, je bil bolan in pripravljen na smrt.
3 Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
Ko je slišal o Jezusu, je k njemu poslal judovske starešine in ga rotil, da bi prišel in ozdravil njegovega služabnika.
4 Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
Ko so prišli k Jezusu, so ga takoj iskreno rotili, rekoč: »Vreden je bil, da bi to storil zanj,
5 saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
kajti rad ima naš narod in sinagogo nam je zgradil.«
6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
Potem je Jezus odšel z njimi. In ko je bil torej nedaleč od hiše, je stotnik k njemu poslal prijatelje, rekoč mu: »Gospod, ne delaj si sitnosti, kajti nisem vreden, da bi stopil pod mojo streho,
7 Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
zato se tudi nisem imel za vrednega, da bi prišel k tebi, toda reci besedo in moj služabnik bo ozdravljen.
8 Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
Kajti tudi sam sem človek, postavljen pod oblast. Pod seboj imam vojake in nekomu rečem: ›Pojdi, ‹ in gre, in drugemu: ›Pridi‹ in pride, in svojemu služabniku: ›Naredi to, ‹ in to stori.«
9 Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
Ko je Jezus slišal te besede, se je začudil nad njim in se obrnil ter rekel množici, ki mu je sledila: »Povem vam: ›Nisem našel tako velike vere, ne, niti v Izraelu ne.‹«
10 Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
In tisti, ki so bili poslani, so se vrnili k hiši in našli služabnika, ki je bil bolan, zdravega.
11 Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
Pripetilo se je dan kasneje, da je odšel v mesto, imenovano Nain in z njim so odšli mnogi izmed njegovih učencev ter veliko ljudi.
12 Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
Ko je torej prišel blizu k mestnim velikim vratom, glej, je bil ven odnesen mrtev človek, edini sin njegove matere in ta je bila vdova; in z njo je bilo veliko ljudi iz mesta.
13 Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
Ko jo je Gospod zagledal, je imel sočutje do nje in ji je rekel: »Ne jokaj.«
14 Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
Prišel je in se dotaknil mrtvaškega odra, in tisti, ki so ga nosili, so mirno stali. In rekel je: »Mladenič, rečem ti: ›Vstani.‹«
15 Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
In ta, ki je bil mrtev, se je usedel in začel govoriti. In izročil ga je njegovi materi.
16 Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
Strah je prišel na vse in slavili so Boga, rekoč, da je med nami vstal velik prerok in da je Bog obiskal svoje ljudi.
17 Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
In ta govorica o njem je šla naprej po vsej celotni Judeji in naokoli po vsem celotnem področju.
18 Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
In Janezovi učenci so mu povedali o vseh teh stvareh.
19 Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
In Janez je k sebi poklical dva izmed svojih učencev in ju poslal k Jezusu, rekoč: »Ali si ti tisti, ki naj bi prišel? Ali [naj] pričakujemo drugega?«
20 Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
Ko sta moža prišla k njemu, sta rekla: »Janez Krstnik naju je poslal k tebi, rekoč: ›Ali si ti tisti, ki naj bi prišel? Ali [naj] pričakujemo drugega?‹«
21 A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
In v tej isti uri je mnoge ozdravil njihovih slabotnosti in nadlog ter od zlih duhov, in mnogim, ki so bili slepi, je dal vid.
22 Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
Potem jima Jezus odgovori in reče: »Pojdita svojo pot in povejta Janezu, kakšne stvari sta videla in slišala: kako slepi vidijo, hromi hodijo, gobavi so očiščeni, gluhi slišijo, mrtvi so obujeni, revnim je oznanjen evangelij.
23 Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
In blagoslovljen je, kdorkoli se ne bo spotaknil ob mene.«
24 Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
In ko sta Janezova poslanca odšla, je množici začel govoriti glede Janeza: »Kaj ste odšli ven v divjino, da vidite? Trst, ki se maje z vetrom?
25 Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
Toda kaj ste odšli ven, da vidite? Človeka, oblečenega v mehka oblačila? Glejte, tisti, ki so krasno oblečeni in žive prefinjeno, so na kraljevih dvorih.
26 Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
Toda kaj ste odšli ven, da vidite? Preroka? Da, povem vam in veliko več kakor preroka.
27 Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
To je on, o katerem je pisano: ›Glej, svojega poslanca pošljem pred tvoj obraz, ki bo pripravil tvojo pot pred teboj.‹
28 Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
Kajti povem vam: ›Med temi, ki so rojeni iz žensk, ni večjega preroka kakor Janez Krstnik, toda kdor je v Božjem kraljestvu najmanjši, je večji od njega.‹«
29 Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
In vsi ljudje, ki so ga slišali in davkarji, so resničnost Boga opravičili s tem, da so se krstili z Janezovim krstom.
30 Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
Toda farizeji in izvedenci v postavi so zavrnili nasvet Boga, sami zoper sebe, tako da se mu niso dali krstiti.
31 Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
In Gospod je rekel: »S kom naj torej primerjam ljudi tega rodu? In čemú so podobni?
32 Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
Podobni so otrokom, sedečim na trgu, ki kličejo drug drugemu ter govorijo: ›Piskali smo vam, pa niste plesali; objokovali smo vam, pa niste jokali.‹
33 Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
Kajti Janez Krstnik je prišel [in] niti ni jedel kruha niti ni pil vina; vi pa pravite: ›Hudiča ima.‹
34 Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
Sin človekov je prišel in jé ter pije; vi pa pravite: ›Glejte, požrešen človek in vinski bratec, prijatelj davkarjev in grešnikov!‹
35 Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
Toda modrost je opravičena po vseh svojih otrocih.«
36 Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
Eden izmed farizejev pa ga je prosil, da bi lahko jedel z njim. In odšel je v farizejevo hišo ter se usedel k obedu.
37 Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
In glej, ko je ženska, ki je bila v mestu grešnica, spoznala, da je Jezus sedel v farizejevi hiši pri obedu, je prinesla alabastrno škatlo mazila
38 Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
ter jokajoč od zadaj pristopila k njegovim stopalom in njegova stopala začela umivati s solzami in jih brisati z lasmi svoje glave in poljubljala je njegova stopala ter jih mazilila z mazilom.
39 Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
Ko je torej to videl farizej, ki ga je povabil, si je rekel sam pri sebi, rekoč: »Če bi bil ta človek prerok, bi vedel, kdo in kakšne vrste je ta ženska, ki se ga dotika, kajti grešnica je.«
40 Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
In Jezus mu odgovori ter reče: »Simon, nekaj ti imam povedati.« On pa reče: »Učitelj, povej.«
41 Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
»Bil je nek upnik, ki je imel dva dolžnika. Eden mu je bil dolžan petsto denarjev, drugi pa petdeset.
42 Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
In ko nista imela nič, s čimer bi plačala, jima je obema odkrito odpustil. Povej mi torej, kateri izmed njiju ga bo bolj ljubil?«
43 Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
Simon je odgovoril in rekel: »Domnevam, da tisti, ki mu je več odpustil.« On pa mu je rekel: »Pravilno si presodil.«
44 Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
In obrnil se je k ženski ter rekel Simonu: »Vidiš to žensko? V tvojo hišo sem vstopil, pa mi nisi dal vode za moja stopala, toda ona je moja stopala umila s solzami in jih obrisala z lasmi svoje glave.
45 Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
Nisi mi dal poljuba, toda odkar sem vstopil, ta ženska ni prenehala poljubljati mojih stopal.
46 Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
Moje glave nisi mazilil z oljem, toda ta ženska je moja stopala mazilila z mazilom.
47 Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
Zato ti pravim: ›Njeni grehi, ki jih je mnogo, so odpuščeni, ‹ kajti veliko je ljubila, toda komur je malo oproščeno, ta malo ljubi.«
48 Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
Njej pa je rekel: »Tvoji grehi so odpuščeni.«
49 Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
In tisti, ki so pri obedu sedeli z njim, so v sebi začeli govoriti: »Kdo je ta, da tudi grehe odpušča?«
50 Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”
In ženski je rekel: »Tvoja vera te je rešila, pojdi v miru.«

< Luka 7 >