< Luka 6 >

1 Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci.
One Sabbath while Jesus was walking through grainfields, his disciples began picking some heads of grain, rubbing them in their hands, and eating them.
2 Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, “Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?”
Some of the Pharisees questioned him, asking, “Why are you doing what is not permitted on the Sabbath?”
3 Yesu ya amsa masu, ya ce, “Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi?
Jesus replied, “Have you never read what David did when he and his men were hungry?
4 Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci.”
How he went into the house of God and took the consecrated bread? He ate it, and gave it to his men too. That's not permitted either. The consecrated bread is only for the priests.”
5 Sai ya ce masu, “Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci.”
Then he told them, “The Son of man is Lord of the Sabbath.”
6 Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye.
On another Sabbath he went into the synagogue to teach. A man was there with a crippled right hand.
7 Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba.
The religious teachers and the Pharisees were observing Jesus closely to see if he would heal on the Sabbath. They wanted to find something to accuse him of.
8 Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, “Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a.” Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.
But Jesus knew what was in their minds. He told the man with the crippled hand, “Get up, and stand here in front of everyone.” The man got up and stood there.
9 Yesu ya ce masu, “Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi?
Then Jesus turned to them and said, “Let me ask you a question. Is it legal to do good on the Sabbath, or to do bad? To save life, or to destroy it?”
10 Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, “Mika hannunka.” Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye.
He looked round at all of them there. Then he said to the man, “Hold out your hand.” The man did so, and his hand became like new.
11 Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.
But they flew into a rage, and began to discuss what they could do to Jesus.
12 Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah.
One day shortly after, Jesus went up a mountain to pray. He remained there all night, praying to God.
13 Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su “Manzanni.”
When morning came he called together his disciples, and chose twelve of them. These are the names of the apostles:
14 Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus,
Simon (also called Peter by Jesus), Andrew his brother, James, John, Philip, Bartholomew,
15 Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu,
Matthew, Thomas, James the son of Alphaeus, Simon the Revolutionary,
16 da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.
Judas the son of James, and Judas Iscariot (who became a traitor).
17 Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon.
Jesus went back down the mountain with them, and stopped at a place where there was some flat ground. There a crowd made up of his disciples and many other people from all over Judea, Jerusalem, and the sea coast of Tyre and Sidon, had gathered to listen to him and to be cured from their diseases.
18 Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa.
Those who were troubled by evil spirits were also healed.
19 Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.
Everyone in the crowd tried to touch him, because power was coming out from him and healing them all.
20 Sai ya dubi almajiransa ya ce, “Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne.
Looking at his disciples, Jesus told them,
21 Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.
“How happy are you who are poor, for the kingdom of God is yours. How happy are you who are hungry now, for you will eat all you need. How happy are you who are weeping now, for you will laugh.
22 Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum.
How happy are you when people hate you, exclude you, insult you, and curse your name as evil because of me, the Son of man.
23 Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
When that day comes, be happy. Jump for joy, for great is your reward in heaven. Don't forget their forefathers mistreated the prophets just like this.
24 Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku.
But how sad are you who are rich, for you have already received your reward.
25 Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
How sad are you who are full now, for you will become hungry. How sad are you who laugh now, for you will mourn and cry.
26 Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
How sad are you when everyone praises you. Don't forget that their forefathers praised false prophets just like this.
27 Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
But I say to those of you who are listening: Love your enemies. Do good to those who hate you.
28 Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
Bless those who curse you. Pray for those who mistreat you.
29 Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.
If someone hits you on one cheek, turn the other cheek. If someone takes your coat, don't prevent them taking your shirt.
30 Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
Give to anyone who asks you. If someone takes something from you, don't ask for it back.
31 Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan.
Do to others what you want them to do to you.
32 Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su.
If you love those who love you, why should you deserve any credit for that? Even sinners love those who love them.
33 Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan.
If you do good to those who do good to you, why should you deserve any credit for that either? Sinners do that as well.
34 Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.
If you lend money expecting to be repaid, why should you deserve any credit for that? Sinners lend money to other sinners as well, expecting to be repaid what they loaned.
35 Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane.
No: love your enemies, do good to them, and lend without expecting to be repaid anything. Then you will receive a great reward, and you will be children of the Most High God, for he is kind to ungrateful and wicked people.
36 Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.
Be compassionate, just as your Father is compassionate.
37 Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.
Don't judge, and you won't be judged; don't condemn, and you won't be condemned; forgive, and you'll be forgiven;
38 Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.
give, and you will be given generously in return. When what you're given is measured out, it's pressed down so more can be added, spilling out over the top, pouring into your lap! For how much you give will determine how much you receive.”
39 Sai ya sake basu wani misali, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba?
Then he illustrated the point: “Can a blind person lead another? Wouldn't they both fall into a ditch?
40 Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.
Do students know more than the teacher? Only when they've learned everything: then they will be like their teacher.
41 Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba?
Why are you so worried about the speck that's in your brother's eye when you don't even notice the plank that's in your own eye?
42 Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.
How can you say to your brother, ‘Brother, let me take out the speck that's in your eye,’ when you don't even see the plank that's in your own eye? Hypocrite! Take out the plank from your own eye first, and then you'll be able to see well enough to take out the speck from your brother's eye.
43 Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya.
A good tree doesn't produce bad fruit, and a bad tree doesn't produce good fruit.
44 Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.
You recognize a tree by the fruit it produces. You don't pick figs from thorn bushes, or harvest grapes from brambles.
45 Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.
Good people produce what's good from the good things they value that they have stored inside them. Bad people produce what's bad from the bad things they have stored inside them. What fills people's minds spills out in what they say.
46 Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta?
So why do you bother to call me, ‘Lord, Lord,’ when you don't do what I say?
47 Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake.
I'll give you an example of someone who comes to me, hears my instructions, and follows them.
48 Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.
That person is like a man building a house. He digs down deep and lays the foundations on solid rock. When the river bursts its banks and the floodwater breaks against the house it's not damaged because it's built so well.
49 Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.
The person who hears me but doesn't do what I say is like a man who builds a house without foundations. When the floodwater breaks against the house it collapses immediately, completely destroyed.”

< Luka 6 >