< Luka 5 >

1 Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
Linu chikwa chitahala, Mukuti vantu vava kungeene kuzimbuluka Jesu ni kutekeleza linzwi lye Ireza, mi avali kuzimene he iyambezi lya Geneserate.
2 Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
Chavona mato ovele ni avakwitilwe he rizo lye iyambezi. bayambi civava kuzwile mwa teni mi vava kwete kushanza tunyandi twavo.
3 Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
Jesu chechira muvumwi bwato, vuvali bwa Simone, chamucho kuti avusikule chivakazana kuzwa ha hamutunda. Chekala hansi ni ku luta vantu nena mubwato.
4 Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
Hamana kuwamba, cha wamba kwa Simone, “Twale bwato mumenzi male mi musohele tunyandi muchese.”
5 Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
Simone chetaba ni kucho “Simwine twatenda masiku onse, kakwina chitwa chesa, kono cha linzwi lyako, munisohele tunyandi.”
6 Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
Hava chita bulyo, chiva kunganya impalo ingi ye nswi, mane tunyandi twavo tuva kuhaloka.
7 Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
chibawambila ba mwavo mubwato bumwi kuti beze zeba vava tuse. Chiveza ni kwizuza mato onse ovele, linu niva tanga kumina.
8 Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
Kono Simone Pitorosi, havona vulyo, cha wa cha mazwi a Jesu chati, “Zwe kwangu kakuti ni muntu ni muvi, Simwine.”
9 Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
Kakuti avakomoketwe, mane nivonse vavali kwina naye, haku cheswa kwe nswi zivava hindi.
10 Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
Aha kuva kwina Jakovo ni Johani, vavali vaanaswisu va Zevedia vavali kusevelisana ni Simone. Mi Jesu chati kwa Simone “Kanji utiyi, kakuti kuzwa hanu mo mochese vantu.”
11 Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
Haba leta mato avo hansi, civa siya zintu zonse niku mwi chilila.
12 Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
Hakuva kuti avali kwina imwi toropo, mukwame yabezwile vutuku bwe mbingwa mwavena. Havona Jesu, cha wa cha chifateho ni ku mukumbila, nacho, “Simwine, haiva usaka uwola kuni joloza.”
13 Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
mi Jesu cha wolola iyanza lyakwe nikumu kwata, nawamba, “Nisaka jolole.” mi haho bulyo imbingwa yakwe chiya zwa kwali.
14 Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
Cha mulaela kuti sanzi awambili muntu, kono cha mucho kuti, “Liyendeze, mi ukalivonahaze kuba purisita mi ukatambike chitabelo cha ku jolozwa kwako, kuya ke taelo ya Mushe, ive vushupi kubali.”
15 Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
Kono ikande liamana naye chi lya yenda iñuwa, mi vungi bwa vantu chiva keza hamwina kwiza kumuzuwa na luta, mane nikuhozwa matuku abo.
16 Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
Kono inako ni inako cha zwa nikuya muzivaka zili mumatongo nikuka lapela.
17 Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
Chikwa sika limwi zuva mwawo mazuva lyava kwete kuluta, mi kuvali kwina Mafarisi ni valuti va mulao vavali kwi kele mwateni kuzwila muminzi mingi ichinchana muzikiliti za Galileya ni Judeya, mane ni mwi tolopo ya Jerusalema. Ziho za Simwine zivali kwina naye za kuhoza.
18 A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
Lyahanu vamwi vakwame chivakeza, vavali kuhindite muntu yo lwala vutuku bwaku zuminina ha vulo, vavali kusaka mahitilo a kumwinjilika mukati ni kuka mulalika havusu bwa Jesu.
19 Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
Kana vavali kuwola kuwana mahitilo o kumwinjilika mukati chevaka lya vantu vangi, linu chiva ya hewulu lya chituwa ni ku sezumwina mukwame hateni, havulo bwakwe, mukati ka vantu, hene havusu bwa Jesu.
20 Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
Chakuvona kuzumina kwavo, Jesu chati, “mukwame, zivi zako chiza swalelwa we.”
21 Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
Va ñoli ni ma Farisi chivatanga kuli vuza ichi, nivati, “Njeni uzu yo wamba cha kunyansiliza? Njeni yowola kuswalela vuvi konji Ireza yeyena?”
22 Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
Kono Jesu, chalemuha zivavali kuhupula, chetava nikuwamba kuvali, “Chinzi hamukwete kuli vuza vulyo mwinkulo zenu,
23 Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
Njechihi chihuva kukuwamba, 'Zibi zako chiza swalelwa,' nikuta kuti 'zimane uyende?'
24 Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
Kono kuti mwizive kuti Mwana Muntu wina inkamaiso zakuswalela zivi hansi, Ni wamba kwako, zimane, 'Hinde vulo bwako mi uyende kwinzuvo yako.'”
25 Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
Haho vulyo cha zimana havusu bwavo ni kunyemuna vulo hava lele. Chavola kwinzuvo yakwe, nakavu kuchenchelela Ireza.
26 Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
Vonse vavakomoketwe niku chenchelela Ireza. Vave zwile kutiya, ni vati “Twavona zintu zihitilize sunu.”
27 Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
Hakumana kupangahala izi zintu, Jesu cha zwa mwateni umo mi avavoni Mutelisi we zina lya Levi nekele mwi tente lya kutambwila mitelo. Chamuta kuti, “Ni chilile.”
28 Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
Linu Levi cha zimana ni kumwi chilila, kusiya zintu zonse kuma sule.
29 Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
Linu Levi cha ha Jesu zilyo zingi munzuvo yakwe. Muvali kwina vatelisi vangi mwateni ni vantu vamwi vavali shamine he ntafule mi niva kwete kulya navo.
30 Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
Kono Vafarisi ni va ñoli vavo vavakwete kuvilela kuvalutwana vakwe, “chivati, Chinzi hamulya ni kunywa niva telisi niva vantu vachita vuvi?”
31 Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
Jesu cha vetava, “Vantu vasa lwali kavasaki musiliki, konji balwala nji musaka.
32 Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
Kena nivakezili kusumpa vantu vashiyeme kuku vaka, kono kusumpa vachita zivi ku ku vaka.
33 Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
Chivawamba kwali, “inako ni nako, valutwana va Johani valinyimanga zilyo niku lapela, ni ba lutwana vava Falisi vachita vulyo navo, kono va lutwana vako valya niku nywa.”
34 Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
Jesu chawamba kuvali, “Kana kwina yo wola kuwambila vena hamukiti wa musesi kuti vali nyime zilyo musesi nasina navo?”
35 Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
Kono mazuva akeza hete nazwiswe kuvali musesi, mi aho kavali nyime zilyo.”
36 Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
Linu Jesu cha wamba che huko kuvali. “Kakwina muntu yohalula isila hachizwato chihya niku lukila hesila ikulukulu. Mi hachita vulyo, mwahalule chizwato chihya, mi kasila kazwa ha chizwato chihya kete kaswanele ha chizwato chikulukulu.
37 Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
Kakwina yo vika i waine ihya muzivikiro ze waine ze dalo chikulukulu. Mi hachita vulyo i wine ihya muiñatule madalo, Mi iwaine muitike. Mi zivikilo ze wine ze dalo muziñatuke.
38 Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
Kono i waine ihya iswanela kubikwa muzibikilo zedalo ziteketeke.
39 Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”
Mi kakwina yo chita kuti hamana kunywa iwaine yakale yosaka ihya, kakuti ucho kuti, “Yakale ina butuka.”

< Luka 5 >