< Luka 5 >

1 Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
AND it came to pass, as the multitude were thronging upon him, in order to hear the word of God, that he was standing by the lake of Gennesaret:
2 Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
and he saw two vessels a-ground near the lake: but the fishermen were gone out of them, and washing their nets.
3 Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
Then he went on board one of the vessels, which was Simon’s, and desired him to put off a little from the land: and sitting down, he taught the multitudes out of the vessel.
4 Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
And when he ceased speaking, he said to Simon, Go off into deep water, and shoot your nets for a draught.
5 Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
And Simon answering, said unto him, Sir, we have been toiling all night, and have taken nothing: but at thy command I will shoot the net.
6 Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
And having done so, they inclosed a prodigious multitude of fishes; and their net was broken.
7 Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
And they made signals to their partners in the other vessels, that they should come to their assistance. And they came, and filled both the vessels, so that they were ready to founder.
8 Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
Then Simon Peter seeing it, fell down on his knees before Jesus, saying, Go from me; for I am a sinful man, O Lord!
9 Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
For amazement had seized on him, and on all who were with him, at the draught of fishes which they had taken:
10 Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
as also on James and John the sons of Zebedee, who were partners with Simon. And Jesus said to Simon, Fear not: henceforward thou shalt catch men.
11 Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
And when they had brought their vessels on shore, they left all, and followed him.
12 Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
And it came to pass as he was just at one of the cities, behold, a man full of leprosy! and seeing Jesus, he fell on his face, and besought him, saying, Lord, if thou wilt, thou canst make me clean.
13 Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
And he stretching out his hand touched him, saying, I will: be thou cleansed. And instantly the leprosy departed from him.
14 Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
And he commanded him to tell no man: but go shew thyself to the priest, and offer for thy purification, as Moses enjoined, for a testimony unto them.
15 Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
Now the discourse concerning him more and more spread through the country: and vast multitudes came together to hear him, and to be cured by him of their disorders.
16 Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
But he himself was in the desert for retirement and prayer.
17 Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
And on a certain day it happened that he was teaching, and there were sitting Pharisees, and doctors of the law, who had come from every town of Galilee, and Judea, and Jerusalem: and the power of the Lord for healing them was exercised.
18 A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
And behold, men carried on a couch a man who was a paralytic; and sought to bring him into the house, and to place him before him.
19 Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
And not discovering by what means they could introduce him, because of the crowd, they went up to the roof, and through the tiling let him down with his little couch into the midst, before Jesus.
20 Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
And seeing their faith, he saith to him, Man, thy sins are forgiven thee.
21 Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
And the scribes and Pharisees began to reason, saying, Who is this that speaketh blasphemies? Who can forgive sins but God alone?
22 Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
And Jesus knowing their reasoning, in reply said to them, Why do ye reason in your hearts?
23 Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
for which is the easier? to say, Thy sins are forgiven; or to say, Arise and walk?
24 Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
But that ye may know that the Son of man hath authority upon earth to forgive sins, (he saith to the paralytic, ) I say to thee, Arise, and take up thy couch, and go into thy house.
25 Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
And instantly he rose up before them, took up that on which he had lain, and went away to his house, giving glory to God.
26 Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
And an extacy of admiration seized upon them all, and they glorified God; and they were filled with awe, saying, We have seen wondrously strange things to-day.
27 Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
And after these things he went out, and saw a farmer of the taxes, named Levi, sitting at the custom-house: and he said unto him, Follow me.
28 Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
And leaving all behind, he rose, and followed him.
29 Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
And Levi made him a great entertainment at his house and there was a great number of publicans and others, sitting at table with them.
30 Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
And their scribes and Pharisees murmured against his disciples, saying, Why do ye eat and drink with publicans and sinners?
31 Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
And Jesus answering said unto them, They who are well, have no need of a physician: but they who have illness.
32 Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
I came not to call righteous men, but sinners, to repentance.
33 Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
Then said they unto him, Why do the disciples of John observe frequent fasts, and make prayers; but thine are eating and drinking?
34 Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
And he said unto them, Can you make the children of the bridechamber fast, as long as the bridegroom is with them?
35 Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
But the days will come, when the bridegroom shall be taken away from them, then shall they fast in those days.
36 Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
Then he spake a parable unto them, No man putteth a patch of new cloth on an old garment; but if otherwise, both the new makes a rent, and the patch from the new is not of a piece with the old.
37 Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
And no man putteth new wine into old bottles; for if he doth, the new wine will burst the bottles, and it will itself be spilled, and the bottles be destroyed.
38 Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
But new wine should be put into new bottles; then both are preserved.
39 Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”
And no man drinking old wine, immediately desires new: for he saith, The old is better.

< Luka 5 >