< Luka 4 >

1 Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
And Jesus, full of the Holy Spirit, turned back from the Jordan, and was brought in the Spirit to the wilderness,
2 kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
forty days being tempted by the Devil, and he did not eat anything in those days, and they having been ended, he afterward hungered,
3 Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
and the Devil said to him, 'If Son thou art of God, speak to this stone that it may become bread.'
4 Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
And Jesus answered him, saying, 'It hath been written, that, not on bread only shall man live, but on every saying of God.'
5 Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
And the Devil having brought him up to an high mountain, shewed to him all the kingdoms of the world in a moment of time,
6 Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
and the Devil said to him, 'To thee I will give all this authority, and their glory, because to me it hath been delivered, and to whomsoever I will, I do give it;
7 Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
thou, then, if thou mayest bow before me — all shall be thine.'
8 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
And Jesus answering him said, 'Get thee behind me, Adversary, for it hath been written, Thou shalt bow before the Lord thy God, and Him only thou shalt serve.'
9 Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
And he brought him to Jerusalem, and set him on the pinnacle of the temple, and said to him, 'If the Son thou art of God, cast thyself down hence,
10 Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
for it hath been written — To His messengers He will give charge concerning thee, to guard over thee,
11 kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
and — On hands they shall bear thee up, lest at any time thou mayest dash against a stone thy foot.'
12 Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
And Jesus answering said to him — 'It hath been said, Thou shalt not tempt the Lord thy God.'
13 Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
And having ended all temptation, the Devil departed from him till a convenient season.
14 Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
And Jesus turned back in the power of the Spirit to Galilee, and a fame went forth through all the region round about concerning him,
15 Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
and he was teaching in their synagogues, being glorified by all.
16 Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
And he came to Nazareth, where he hath been brought up, and he went in, according to his custom, on the sabbath-day, to the synagogue, and stood up to read;
17 An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
and there was given over to him a roll of Isaiah the prophet, and having unfolded the roll, he found the place where it hath been written:
18 “Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
'The Spirit of the Lord [is] upon me, Because He did anoint me; To proclaim good news to the poor, Sent me to heal the broken of heart, To proclaim to captives deliverance, And to blind receiving of sight, To send away the bruised with deliverance,
19 in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
To proclaim the acceptable year of the Lord.'
20 Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
And having folded the roll, having given [it] back to the officer, he sat down, and the eyes of all in the synagogue were gazing on him.
21 Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
And he began to say unto them — 'To-day hath this writing been fulfilled in your ears;'
22 Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
and all were bearing testimony to him, and were wondering at the gracious words that are coming forth out of his mouth, and they said, 'Is not this the son of Joseph?'
23 Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
And he said unto them, 'Certainly ye will say to me this simile, Physician, heal thyself; as great things as we heard done in Capernaum, do also here in thy country;'
24 Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
and he said, 'Verily I say to you — No prophet is accepted in his own country;
25 Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
and of a truth I say to you, Many widows were in the days of Elijah, in Israel, when the heaven was shut for three years and six months, when great famine came on all the land,
26 Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
and unto none of them was Elijah sent, but — to Sarepta of Sidon, unto a woman, a widow;
27 Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
and many lepers were in the time of Elisha the prophet, in Israel, and none of them was cleansed, but — Naaman the Syrian.'
28 Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
And all in the synagogue were filled with wrath, hearing these things,
29 Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
and having risen, they put him forth without the city, and brought him unto the brow of the hill on which their city had been built — to cast him down headlong,
30 Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
and he, having gone through the midst of them, went away.
31 Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
And he came down to Capernaum, a city of Galilee, and was teaching them on the sabbaths,
32 Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
and they were astonished at his teaching, because his word was with authority.
33 A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
And in the synagogue was a man, having a spirit of an unclean demon, and he cried out with a great voice,
34 “Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
saying, 'Away, what — to us and to thee, Jesus, O Nazarene? thou didst come to destroy us; I have known thee who thou art — the Holy One of God.'
35 Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
And Jesus did rebuke him, saying, 'Be silenced, and come forth out of him;' and the demon having cast him into the midst, came forth from him, having hurt him nought;
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
and amazement came upon all, and they were speaking together, with one another, saying, 'What [is] this word, that with authority and power he doth command the unclean spirits, and they come forth?'
37 Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
and there was going forth a fame concerning him to every place of the region round about.
38 Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
And having risen out of the synagogue, he entered into the house of Simon, and the mother-in-law of Simon was pressed with a great fever, and they did ask him about her,
39 Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
and having stood over her, he rebuked the fever, and it left her, and presently, having risen, she was ministering to them.
40 Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
And at the setting of the sun, all, as many as had any ailing with manifold sicknesses, brought them unto him, and he on each one of them [his] hands having put, did heal them.
41 Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
And demons also were coming forth from many, crying out and saying — 'Thou art the Christ, the Son of God;' and rebuking, he did not suffer them to speak, because they knew him to be the Christ.
42 Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
And day having come, having gone forth, he went on to a desert place, and the multitudes were seeking him, and they came unto him, and were staying him — not to go on from them,
43 Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
and he said unto them — 'Also to the other cities it behoveth me to proclaim good news of the reign of God, because for this I have been sent;'
44 Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.
and he was preaching in the synagogues of Galilee.

< Luka 4 >