< Luka 4 >

1 Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
Then Jesus, being full of the Holy Spirit, returned from the Jordan River, and was led by the Spirit in the wilderness,
2 kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
where for forty days he was tempted by the devil. He ate nothing during those days, and at the end of that time he was hungry.
3 Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
The devil said to him, “If you are the Son of God, command this stone to become bread.”
4 Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
Jesus answered him, “It is written, 'Man does not live on bread alone.'”
5 Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
Then the devil led Jesus up and showed him all the kingdoms of the world in an instant of time.
6 Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
The devil said to him, “I will give to you all this authority and all their splendor, for they have been given to me, and I can give it to anyone I want.
7 Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
So then, if you will bow down and worship me, it will be yours.”
8 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
But Jesus answered and said to him, “It is written, 'You will worship the Lord your God, and you will serve only him.'”
9 Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
Then the devil led Jesus to Jerusalem and put him on the very highest point of the temple building, and said to him, “If you are the Son of God, throw yourself down from here.
10 Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
For it is written, 'He will give orders to his angels regarding you, to protect you,'
11 kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
and, 'They will lift you up in their hands, so that you will not strike your foot against a stone.'”
12 Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
Answering him, Jesus said, “It is said, 'Do not put the Lord your God to the test.'”
13 Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
When the devil had finished testing Jesus, he went away and left him until another time.
14 Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
Then Jesus returned to Galilee in the power of the Spirit, and news about him spread throughout the entire surrounding region.
15 Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
Then he began to teach in their synagogues and he was praised by all.
16 Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
He came into Nazareth, where he had been raised, and as was his custom, he entered the synagogue on the Sabbath day and he stood up to read aloud.
17 An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
The scroll of the prophet Isaiah was handed to him. He opened the scroll and found the place where it was written,
18 “Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
“The Spirit of the Lord is upon me, because he anointed me to tell good news to the poor. He has sent me to proclaim freedom to the captives, and recovery of sight to the blind, to set free those who are oppressed,
19 in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
to proclaim the year of the Lord's favor.”
20 Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
Then he rolled up the scroll, gave it back to the attendant, and sat down. The eyes of all in the synagogue were fixed on him.
21 Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
He began to speak to them, “Today this scripture has been fulfilled in your hearing.”
22 Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
Everyone there spoke well of him and they were amazed at the gracious words which were coming out of his mouth, and they asked, “Is this not the son of Joseph?”
23 Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
He said to them, “Surely you will say this proverb to me, 'Doctor, heal yourself. Whatever we heard that you did in Capernaum, do the same in your hometown.'”
24 Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
But he said, “Truly I say to you, no prophet is received in his own hometown.
25 Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
But in truth I tell you that there were many widows in Israel during the time of Elijah, when the sky was shut up for three years and six months, and a great famine came upon all the land.
26 Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
But Elijah was sent to none of them, but only to Zarephath in Sidon, to a widow living there.
27 Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
There were many lepers in Israel during the time of Elisha the prophet, but none of them were healed except Naaman the Syrian.”
28 Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
All the people in the synagogue were filled with rage when they heard these things.
29 Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
They got up, forced him out of the town, and led him to the cliff of the hill on which their town was built, so they might throw him off the cliff.
30 Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
But he passed through the middle of them and he went to another place.
31 Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
Then he went down to Capernaum, a city in Galilee, and he began to teach them on the Sabbath.
32 Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
They were astonished at his teaching, because he spoke with authority.
33 A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
Now in the synagogue there was a man who had the spirit of an unclean demon, and he cried out with a loud voice,
34 “Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
“Ah! What do we have to do with you, Jesus of Nazareth? Have you come to destroy us? I know who you are—the Holy One of God!”
35 Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
Jesus rebuked the demon, saying, “Do not speak! Come out of him!” When the demon had thrown the man down in the middle of them, he came out of him, and did not harm him in any way.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
All the people were very amazed, and they kept talking about it with one another. They said, “What kind of words are these? He commands the unclean spirits with authority and power and they come out.”
37 Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
So news about him began to spread into every part of the surrounding region.
38 Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
Then Jesus left the synagogue and entered into the house of Simon. Now Simon's mother-in-law was suffering with a high fever, and they pleaded with him on her behalf.
39 Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
So he stood over her and rebuked the fever, and it left her. Immediately she got up and started serving them.
40 Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
When the sun was setting, people brought to Jesus everyone who was sick with various kinds of diseases. He laid his hands on every one of them and healed them.
41 Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
Demons also came out from many of them, crying out and saying, “You are the Son of God!” Jesus rebuked the demons and would not let them speak, because they knew that he was the Christ.
42 Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
When daybreak came, he went out into a solitary place. Crowds of people were looking for him and came to the place where he was. They tried to keep him from going away from them.
43 Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
But he said to them, “I must also preach the good news about the kingdom of God to many other cities, because this is the reason I was sent here.”
44 Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.
Then he continued to preach in the synagogues throughout Judea.

< Luka 4 >