< Luka 4 >

1 Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
And Jesus, full of the Holy Spirit, came back from the Jordan, and was guided by the Spirit in the waste land
2 kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
For forty days, being tested by the Evil One. And he had no food in those days; and when they came to an end, he was in need of food.
3 Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
And the Evil One said to him, If you are the Son of God, give orders to this stone to become bread.
4 Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
And Jesus made answer to him, It has been said in the Writings, Bread is not man's only need.
5 Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
And he took him up and let him see all the kingdoms of the earth in a minute of time.
6 Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
And the Evil One said, I will give you authority over all these, and the glory of them, for it has been given to me, and I give it to anyone at my pleasure.
7 Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
If then you will give worship to me, it will all be yours.
8 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
And Jesus in answer said to him, It has been said in the Writings, Give worship to the Lord your God, and be his servant only.
9 Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
And he took him to Jerusalem and put him on the highest point of the Temple and said to him, If you are the Son of God, let yourself go down from here; for it is said in the Writings,
10 Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
He will give his angels orders to take care of you:
11 kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
And, In their hands they will keep you up, so that your foot may not be crushed against a stone.
12 Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
And Jesus made answer and said to him, It is said in the Writings, You may not put the Lord your God to the test.
13 Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
And when all these tests were ended the Evil One went away from him for a time.
14 Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
And Jesus came back to Galilee in the power of the Spirit, and the news of him went through all the country round about.
15 Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
And he was teaching in their Synagogues and all men gave him praise.
16 Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
And he came to Nazareth, where he had been as a child, and he went, as his way was, into the Synagogue on the Sabbath, and got up to give a reading.
17 An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
And the book of the prophet Isaiah was given to him and, opening the book, he came on the place where it is said,
18 “Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
The Spirit of the Lord is on me, because I am marked out by him to give good news to the poor; he has sent me to make well those who are broken-hearted; to say that the prisoners will be let go, and the blind will see, and to make the wounded free from their chains,
19 in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
To give knowledge that the year of the Lord's good pleasure is come.
20 Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
And shutting the book he gave it back to the servant and took his seat: and the eyes of all in the Synagogue were fixed on him.
21 Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
Then he said to them, Today this word has come true in your hearing.
22 Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
And they were all giving witness, with wonder, to the words of grace which came from his mouth: and they said, Is not this the son of Joseph?
23 Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
And he said to them, Without doubt you will say to me, Let the medical man make himself well: the things which to our knowledge were done at Capernaum, do them here in your country.
24 Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
And he said to them, Truly I say to you, No prophet is honoured in his country.
25 Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
Truly I say to you, There were a number of widows in Israel in the days of Elijah, when the heaven was shut up for three years and six months and there was no food in the land;
26 Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
But Elijah was not sent to one of them, but only to Zarephath, in the land of Sidon, to a woman who was a widow.
27 Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
And there were a number of lepers in Israel in the time of Elisha the prophet, and not one of them was made clean, but only Naaman the Syrian.
28 Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
And all who were in the Synagogue were very angry when these things were said to them.
29 Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
And they got up and took him out of the town to the edge of the mountain on which their town was, so that they might send him down to his death.
30 Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
But he came through them and went on his way.
31 Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
And he came down to Capernaum, a town of Galilee; and he was giving them teaching on the Sabbath.
32 Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
And they were surprised at his teaching, for his word was with authority.
33 A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
And there was a man in the Synagogue who had an unclean spirit; and he gave a loud cry and said,
34 “Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
Let us be! what have we to do with you, Jesus of Nazareth? have you come to put an end to us? I have knowledge who you are, the Holy One of God.
35 Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
And Jesus said to him, Be quiet, and come out of him. And when the evil spirit had put him down on the earth in the middle of them, he came out of him, having done him no damage.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
And wonder came on them all and they said to one another, What are these words? for with authority and power he gives orders to the evil spirits and they come out.
37 Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
And there was much talk about him in all the places round about.
38 Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
And he got up and went out of the Synagogue and went into the house of Simon. And Simon's wife's mother was very ill with a burning heat; and in answer to their prayers for her
39 Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
He went near her, and with a sharp word he gave orders to the disease and it went away from her; and straight away she got up and took care of their needs.
40 Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
And at sundown all those who had anyone ill with any sort of disease, took them to him, and he put his hands on every one of them and made them well.
41 Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
And evil spirits came out of a number of them, crying out and saying, You are the Son of God. But he gave them sharp orders not to say a word, because they had knowledge that he was the Christ.
42 Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
And when it was day, he came out and went to a waste place; and great numbers of people came looking for him, and they came to him and would have kept him from going away.
43 Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
But he said to them, I have to give the good news of the kingdom of God in other towns, because that is why I was sent.
44 Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.
And he was teaching in the Synagogues of Galilee.

< Luka 4 >