< Luka 3 >

1 A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
En l'an quinze du règne de Tibère César, — Ponce-Pilate étant procurateur de la Judée, — Hérode, tétrarque de la Galilée, —Philippe, son frère, tétrarque de l'Iturée et des terres de la Trachonite, — Lysanias, tétrarque de l'Abilène, —
2 kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
sous le pontificat de Banne et de Kaïphe, la parole de Dieu fut adressée à Jean, fils de Zaccharie, dans le désert.
3 Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
Et Jean s'en alla dans toute la région du Jourdain, prêchant un baptême de repentance pour la rémission des péchés,
4 Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
ainsi que cela est écrit au livre des paroles du prophète Ésaïe: «Une voix crie dans le désert: Préparez la voie du Seigneur, Aplanissez ses sentiers;
5 Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
Toute vallée sera comblée; Toute montagne et toute colline seront abaissées; Les voies tortueuses seront changées en droits chemins; Et les voies rocailleuses en routes unies;
6 kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
Et toute chair verra le salut de Dieu»
7 Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Aux foules qui accouraient pour être baptisées par lui, il disait: «Engeance de vipères, qui vous a appris à fuir la colère à venir?
8 Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
Produisez donc des fruits dignes de la repentance, et n'allez pas dire en vous-mêmes: Nous avons pour père Abraham; car je vous le dis, Dieu peut faire surgir, des pierres que voici, des enfants à Abraham.
9 Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
Déjà la cognée touche la racine des arbres. Tout arbre donc qui ne produit pas de bon fruit, sera coupé et jeté au feu.» —
10 Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
«Qu'avons-nous à faire?» lui demandèrent alors les multitudes.
11 Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
Il leur répondit par ces paroles: «Que celui qui possède deux tuniques en donne une à celui qui n'en a pas et que celui qui a des aliments pour se nourrir fasse de même.»
12 Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
Des publicains vinrent pour être baptisés et lui dirent aussi: «Maître, qu'avons-nous à faire?» —
13 Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
«N'exigez rien de plus, leur répondit-il, que ce qui vous a été prescrit.»
14 Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
Des soldats aussi le questionnèrent: «Et nous, qu'avons-nous à faire?» A eux il dit: «Ne faites violence à personne; ne faites tort à personne; contentez-vous de votre paye.»
15 Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
Le peuple était en suspens; et chacun se demandait, dans le secret de son coeur, si Jean n'était pas peut-être le Christ.
16 Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
Pour répondre à tous, Jean dit: «Moi, je vous baptise d'eau; mais il va venir celui qui est plus puissant que moi; je ne suis pas même digne de délier la courroie de ses sandales; lui, vous baptisera avec l'Esprit saint et le feu.
17 Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
Il a le van dans la main pour nettoyer son aire et rassembler le froment dans son grenier; mais la paille il la brûlera au feu inextinguible.»
18 Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
C'est ainsi qu'il annonçait la Bonne Nouvelle au peuples par des exhortations nombreuses et variées.
19 Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
Le tétrarque Hérode, cependant, ayant été repris par lui tant au sujet d'Hérodiade, femme de son frère, qu'au sujet des mille crimes qu'il avait commis,
20 Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
ajouta encore celui-ci à tous les autres: il fit jeter Jean en prison.
21 Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
Or tout le peuple ayant reçu le baptême, et Jésus aussi ayant été baptisé, il advint que le ciel s'ouvrit, pendant qu'il priait,
22 kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
et que l'Esprit saint descendit sur lui sous une forme corporelle, sous la figure d'une colombe; et une voix vint du ciel: «Tu es mon Fils bien-aimé, en toi je me complais.»
23 Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
Jésus, en ce commencement, avait environ trente ans et passait pour être le fils de Joseph, Fils d'Héli,
24 dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
Fils de Maththath, Fils de Lévi, Fils de Melchi, Fils de Jannaï, Fils de Joseph,
25 dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
Fils de Mattathias, Fils d'Amos, Fils de Naoum, Fils d'Eslei, Fils de Nangaï,
26 dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
Fils de Maath, Fils de Mattathias, Fils de Semeein, Fils de Josech, Fils de Joda,
27 dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
Fils de Joanan, Fils de Rèsa, Fils de Zorobabel, Fils de Salathiel, Fils de Nèrei,
28 dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
Fils de Melchei, Fils d'Addei, Fils de Kosam, Fils de Elmadam, Fils de Hèr,
29 dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
Fils de Jésus, Fils d'Éliézer, Fils de Jorem, Fils de Maththath, Fils de Lévi,
30 dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
Fils de Siméon, Fils de Judas, Fils de Joseph, Fils de Jonam, Fils d'Éliakim, Fils de Méléa,
31 dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
Fils de Menna, Fils de Mattatha, Fils de Natham, Fils de David,
32 dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
Fils de Jessaï, Fils de Jobed, Fils de Boos, Fils de Sala, Fils de Naasson,
33 dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
Fils d'Aminadab, Fils d'Admein, Fils d'Ami, Fils d'Esrom, Fils de Pharès, Fils de Judas,
34 dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
Fils de Jacob, Fils d'Isaac, Fils d'Abraham, Fils de Unira, Fils de Nachor, Fils de Serouch,
35 dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
Fils de Ragau, Fils de Phalek, Fils de Eber, Fils de Sala,
36 dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
Fils de Kainam, Fils d'Arphaxad, Fils de Sein, Fils de Noé, Fils de Lamech,
37 dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
Fils de Mathousalem. Fils d'Enoch, Fils de Jaret, Fils de Meleleèl, Fils de Kainam
38 dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.
Fils d'Enos, Fils de Seth, Fils d'Adam, Fils de Dieu.

< Luka 3 >