< Luka 3 >

1 A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
La quinzième année de l'empire de Tibère César, Ponce Pilate étant gouverneur de la Judée, Hérode, tétrarque de la Galilée, Philippe son frère, tétrarque de l'Iturée et de la province de la Trachonite, et Lysanias; tétrarque d'Abylène,
2 kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
Sous la souveraine sacrificature d'Anne et de Caïphe, la parole de Dieu fut adressée à Jean, fils de Zacharie, dans le désert.
3 Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
Et il vint dans tout le pays des environs du Jourdain, prêchant le baptême de repentance, pour la rémission des péchés;
4 Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
Selon qu'il est écrit au livre des paroles du prophète Ésaïe: Voix de celui qui crie dans le désert: Préparez le chemin du Seigneur, aplanissez ses sentiers.
5 Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
Toute vallée sera comblée, et toute montagne et toute colline sera abaissée, les chemins tortueux seront redressés, et les chemins raboteux seront aplanis;
6 kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
Et toute chair verra le salut de Dieu.
7 Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Il disait donc au peuple qui venait pour être baptisé par lui: Race de vipères, qui vous a appris à fuir la colère à venir?
8 Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
Produisez donc des fruits convenables à la repentance; et ne vous mettez point à dire en vous-mêmes: Nous avons Abraham pour père; car je vous dis que Dieu peut faire naître de ces pierres des enfants à Abraham.
9 Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
Or, la cognée est déjà mise à la racine des arbres. Tout arbre donc qui ne produit pas de bon fruit va être coupé et jeté au feu.
10 Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
Alors le peuple lui demanda: Que ferons-nous donc?
11 Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
Il leur répondit: Que celui qui a deux habits en donne à celui qui n'en a point; et que celui qui a de la nourriture en fasse de même.
12 Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
Il vint aussi des péagers pour être baptisés;
13 Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
Et ils lui dirent: Maître, que ferons-nous? Et il leur dit: N'exigez rien au-delà de ce qui vous a été ordonné.
14 Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
Les gens de guerre lui demandèrent aussi: Et nous, que ferons-nous? Il leur dit: N'usez point de violence ni de tromperie envers personne, mais contentez vous de votre paye.
15 Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
Et comme le peuple était dans l'attente, et que tous se demandaient en leurs cœurs si Jean ne serait point le Christ,
16 Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
Jean prit la parole et dit à tous: Pour moi, je vous baptise d'eau; mais il en vient un plus puissant que moi; et je ne suis pas digne de délier la courroie de ses souliers; c'est lui qui vous baptisera du Saint-Esprit et de feu.
17 Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
Il a son van dans ses mains, il nettoiera parfaitement son aire, et il amassera le froment dans son grenier; mais il brûlera entièrement la paille, au feu qui ne s'éteint point.
18 Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
Il adressait encore plusieurs autres exhortations au peuple, en lui annonçant l'Évangile.
19 Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
Mais Hérode le tétrarque ayant été repris par Jean, au sujet d'Hérodias, femme de Philippe son frère, et de toutes les méchantes actions qu'il avait faites,
20 Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
Ajouta encore à toutes les autres celle de faire mettre Jean en prison.
21 Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
Or, comme tout le peuple se faisait baptiser, Jésus fut aussi baptisé; et pendant qu'il priait, le ciel s'ouvrit,
22 kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
Et le Saint-Esprit descendit sur lui sous une forme corporelle, comme une colombe; et il vint une voix du ciel, qui dit: Tu es mon Fils bien-aimé, en qui j'ai pris plaisir.
23 Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
Et Jésus était âgé d'environ trente ans quand il commença, et il était, comme on le croyait, fils de Joseph, d'Héli,
24 dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
De Matthat, de Lévi, de Melchi, de Janna, de Joseph,
25 dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
De Matthathie, d'Amos, de Nahum, d'Héli, de Naggé,
26 dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
De Maath, de Matthathie, de Semeï, de Joseph, de Juda,
27 dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
De Johanna, de Rhésa, de Zorobabel, de Salathiel, de Néri,
28 dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
De Melchi, d'Addi, de Cosam, d'Elmodam, de Her,
29 dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
De José, d'Éliézer, de Jorim, de Matthat, de Lévi,
30 dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
De Siméon, de Juda, de Joseph, de Jonan, d'Éliakim,
31 dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
De Méléa, de Maïnan, de Matthatha, de Nathan, de David,
32 dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
De Jessé, d'Obed, de Booz, de Salomon, de Naasson,
33 dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
D'Aminadab, d'Aram, d'Esrom, de Pharez, de Juda,
34 dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
De Jacob, d'Isaac, d'Abraham, de Tharé, de Nachor,
35 dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
De Sarug, de Ragaü, de Phaleg, de Héber, de Sala,
36 dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
De Caïnan, d'Arphaxad, de Sem, de Noé, de Lamech,
37 dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
De Mathusala, d'Hénoch, de Jared, de Malaléel, de Caïnan,
38 dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.
D'Énos, de Seth, d'Adam, fils de Dieu.

< Luka 3 >