< Luka 3 >

1 A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, Pontius Pilate being governor of Judea, and Herod being tetrarch of Galilee, and his brother Philip tetrarch of the region of Ituraea and Trachonitis, and Lysanias tetrarch of Abilene,
2 kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
during the high priesthood of Annas and Caiaphas, the word of God came to John, the son of Zacharias, in the wilderness.
3 Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
He came into all the region around the Jordan, preaching the baptism of repentance for remission of sins.
4 Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
As it is written in the book of the words of Isaiah the prophet, “The voice of one crying in the wilderness, ‘Make ready the way of the Lord. Make his paths straight.
5 Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
Every valley will be filled. Every mountain and hill will be brought low. The crooked will become straight, and the rough ways smooth.
6 kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
All flesh will see God’s salvation.’”
7 Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
He said therefore to the multitudes who went out to be baptised by him, “You offspring of vipers, who warned you to flee from the wrath to come?
8 Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
Therefore produce fruits worthy of repentance, and don’t begin to say amongst yourselves, ‘We have Abraham for our father;’ for I tell you that God is able to raise up children to Abraham from these stones!
9 Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
Even now the axe also lies at the root of the trees. Every tree therefore that doesn’t produce good fruit is cut down and thrown into the fire.”
10 Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
The multitudes asked him, “What then must we do?”
11 Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
He answered them, “He who has two coats, let him give to him who has none. He who has food, let him do likewise.”
12 Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
Tax collectors also came to be baptised, and they said to him, “Teacher, what must we do?”
13 Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
He said to them, “Collect no more than that which is appointed to you.”
14 Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
Soldiers also asked him, saying, “What about us? What must we do?” He said to them, “Extort from no one by violence, neither accuse anyone wrongfully. Be content with your wages.”
15 Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
As the people were in expectation, and all men reasoned in their hearts concerning John, whether perhaps he was the Christ,
16 Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
John answered them all, “I indeed baptise you with water, but he comes who is mightier than I, the strap of whose sandals I am not worthy to loosen. He will baptise you in the Holy Spirit and fire.
17 Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
His winnowing fan is in his hand, and he will thoroughly cleanse his threshing floor, and will gather the wheat into his barn; but he will burn up the chaff with unquenchable fire.”
18 Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
Then with many other exhortations he preached good news to the people,
19 Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
but Herod the tetrarch, being reproved by him for Herodias, his brother’s wife, and for all the evil things which Herod had done,
20 Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
added this also to them all, that he shut up John in prison.
21 Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
Now when all the people were baptised, Jesus also had been baptised and was praying. The sky was opened,
22 kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
and the Holy Spirit descended in a bodily form like a dove on him; and a voice came out of the sky, saying “You are my beloved Son. In you I am well pleased.”
23 Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
Jesus himself, when he began to teach, was about thirty years old, being the son (as was supposed) of Joseph, the son of Heli,
24 dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
the son of Matthat, the son of Levi, the son of Melchi, the son of Jannai, the son of Joseph,
25 dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
the son of Mattathias, the son of Amos, the son of Nahum, the son of Esli, the son of Naggai,
26 dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
the son of Maath, the son of Mattathias, the son of Semein, the son of Joseph, the son of Judah,
27 dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
the son of Joanan, the son of Rhesa, the son of Zerubbabel, the son of Shealtiel, the son of Neri,
28 dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
the son of Melchi, the son of Addi, the son of Cosam, the son of Elmodam, the son of Er,
29 dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
the son of Jose, the son of Eliezer, the son of Jorim, the son of Matthat, the son of Levi,
30 dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
the son of Simeon, the son of Judah, the son of Joseph, the son of Jonan, the son of Eliakim,
31 dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
the son of Melea, the son of Menan, the son of Mattatha, the son of Nathan, the son of David,
32 dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
the son of Jesse, the son of Obed, the son of Boaz, the son of Salmon, the son of Nahshon,
33 dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
the son of Amminadab, the son of Aram, the son of Hezron, the son of Perez, the son of Judah,
34 dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
the son of Jacob, the son of Isaac, the son of Abraham, the son of Terah, the son of Nahor,
35 dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
the son of Serug, the son of Reu, the son of Peleg, the son of Eber, the son of Shelah,
36 dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
the son of Cainan, the son of Arphaxad, the son of Shem, the son of Noah, the son of Lamech,
37 dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
the son of Methuselah, the son of Enoch, the son of Jared, the son of Mahalaleel, the son of Cainan,
38 dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.
the son of Enos, the son of Seth, the son of Adam, the son of God.

< Luka 3 >