< Luka 3 >

1 A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Cæsar, Pontius Pilate being governor of Judæa, and Herod being tetrarch of Galilee, and his brother Philip tetrarch of Ituraea and of the region of Trachonitis, and Lysanias the tetrarch of Abilene,
2 kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
Annas and Caiaphas being the high priests, the word of God came unto John the son of Zacharias in the wilderness.
3 Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
And he came into all the country about Jordan, preaching the baptism of repentance for the remission of sins;
4 Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
As it is written in the book of the words of Esaias the prophet, saying, The voice of one crying in the wilderness, Prepare ye the way of the Lord, make his paths straight.
5 Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
Every valley shall be filled, and every mountain and hill shall be brought low; and the crooked shall be made straight, and the rough ways [shall be] made smooth;
6 kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
And all flesh shall see the salvation of God.
7 Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Then said he to the multitude that came forth to be baptized of him, O generation of vipers, who hath warned you to flee from the wrath to come?
8 Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
Bring forth therefore fruits worthy of repentance, and begin not to say within yourselves, We have Abraham to [our] father: for I say unto you, That God is able of these stones to raise up children unto Abraham.
9 Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
And now also the axe is laid unto the root of the trees: every tree therefore which bringeth not forth good fruit is hewn down, and cast into the fire.
10 Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
And the people asked him, saying, What shall we do then?
11 Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
He answereth and saith unto them, He that hath two coats, let him impart to him that hath none; and he that hath meat, let him do likewise.
12 Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
Then came also publicans to be baptized, and said unto him, Master, what shall we do?
13 Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
And he said unto them, Exact no more than that which is appointed you.
14 Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
And the soldiers likewise demanded of him, saying, And what shall we do? And he said unto them, Do violence to no man, neither accuse [any] falsely; and be content with your wages.
15 Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
And as the people were in expectation, and all men mused in their hearts of John, whether he were the Christ, or not;
16 Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
John answered, saying unto [them] all, I indeed baptize you with water; but one mightier than I cometh, the latchet of whose shoes I am not worthy to unloose: he shall baptize you with the Holy Ghost and with fire:
17 Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
Whose fan [is] in his hand, and he will throughly purge his floor, and will gather the wheat into his garner; but the chaff he will burn with fire unquenchable.
18 Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
And many other things in his exhortation preached he unto the people.
19 Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
But Herod the tetrarch, being reproved by him for Herodias his brother Philip’s wife, and for all the evils which Herod had done,
20 Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
Added yet this above all, that he shut up John in prison.
21 Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
Now when all the people were baptized, it came to pass, that Jesus also being baptized, and praying, the heaven was opened,
22 kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
And the Holy Ghost descended in a bodily shape like a dove upon him, and a voice came from heaven, which said, Thou art my beloved Son; in thee I am well pleased.
23 Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
And Jesus himself began to be about thirty years of age, being (as was supposed) the son of Joseph, which was [the son] of Heli,
24 dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
Which was [the son] of Matthat, which was [the son] of Levi, which was [the son] of Melchi, which was [the son] of Janna, which was [the son] of Joseph,
25 dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
Which was [the son] of Mattathias, which was [the son] of Amos, which was [the son] of Naum, which was [the son] of Esli, which was [the son] of Nagge,
26 dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
Which was [the son] of Maath, which was [the son] of Mattathias, which was [the son] of Semei, which was [the son] of Joseph, which was [the son] of Juda,
27 dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
Which was [the son] of Joanna, which was [the son] of Rhesa, which was [the son] of Zorobabel, which was [the son] of Salathiel, which was [the son] of Neri,
28 dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
Which was [the son] of Melchi, which was [the son] of Addi, which was [the son] of Cosam, which was [the son] of Elmodam, which was [the son] of Er,
29 dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
Which was [the son] of Jose, which was [the son] of Eliezer, which was [the son] of Jorim, which was [the son] of Matthat, which was [the son] of Levi,
30 dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
Which was [the son] of Simeon, which was [the son] of Juda, which was [the son] of Joseph, which was [the son] of Jonan, which was [the son] of Eliakim,
31 dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
Which was [the son] of Melea, which was [the son] of Menan, which was [the son] of Mattatha, which was [the son] of Nathan, which was [the son] of David,
32 dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
Which was [the son] of Jesse, which was [the son] of Obed, which was [the son] of Booz, which was [the son] of Salmon, which was [the son] of Naasson,
33 dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
Which was [the son] of Aminadab, which was [the son] of Aram, which was [the son] of Esrom, which was [the son] of Phares, which was [the son] of Juda,
34 dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
Which was [the son] of Jacob, which was [the son] of Isaac, which was [the son] of Abraham, which was [the son] of Thara, which was [the son] of Nachor,
35 dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
Which was [the son] of Saruch, which was [the son] of Ragau, which was [the son] of Phalec, which was [the son] of Heber, which was [the son] of Sala,
36 dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
Which was [the son] of Cainan, which was [the son] of Arphaxad, which was [the son] of Sem, which was [the son] of Noe, which was [the son] of Lamech,
37 dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
Which was [the son] of Mathusala, which was [the son] of Enoch, which was [the son] of Jared, which was [the son] of Maleleel, which was [the son] of Cainan,
38 dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.
Which was [the son] of Enos, which was [the son] of Seth, which was [the son] of Adam, which was [the son] of God.

< Luka 3 >