< Luka 23 >

1 Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus.
Ils se levèrent en masse, et conduisirent Jésus devant Pilate.
2 Suka fara saransa, cewa “Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki.”
Ils se mirent à l'accuser, disant: «Nous avons trouvé cet homme qui poussait notre nation à la révolte, et qui défendait de payer le tribut à César, se prétendant lui-même Messie, Roi.»
3 Bilatus ya tambaye shi, cewa “Shin kaine Sarkin Yahudawa?” Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Haka ka ce.”
Pilate l'interrogea, disant: «Tu es le roi des Juifs?» — «Tu le dis, » lui répondit Jésus.
4 Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, “Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba.”
Pilate dit aux principaux sacrificateurs et à la foule: «Je ne trouve rien de criminel en cet homme.»
5 Amma suka yi ta cewa, “Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri.”
Mais ils insistèrent, disant: «Il agite le peuple, en enseignant par toute la Judée, après avoir commencé par la Galilée, et être venu jusqu'ici.»
6 Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline.
Pilate, entendant nommer la Galilée, demanda si cet homme était Galiléen;
7 Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
et ayant appris qu'il était de la juridiction d'Hérode, il le renvoya à Hérode, qui était aussi à Jérusalem en ces jours-là.
8 Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi.
Hérode eut une grande joie de voir Jésus, car depuis longtemps il en avait le désir, parce qu'il avait entendu parler de lui, et qu'il espérait le voir faire quelque miracle.
9 Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba.
Il lui adressa un grand nombre de questions, mais Jésus ne lui répondit rien.
10 Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
Or les principaux sacrificateurs et les scribes étaient là, qui l'accusaient avec véhémence;
11 Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus.
mais Hérode avec sa garde le traita avec mépris: il le fit revêtir par dérision d'un magnifique manteau, et le renvoya à Pilate.
12 Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).
Le jour même, Pilate et Hérode devinrent amis, d'ennemis qu'ils étaient auparavant.
13 Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar,
Pilate, ayant assemblé les principaux sacrificateurs, les sénateurs et le peuple, leur dit:
14 sai ya ce masu, “Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
«Vous avez traduit devant moi cet homme, comme excitant le peuple à la révolte, et, après l'avoir interrogé en votre présence, je ne l'ai trouvé coupable d'aucun des crimes dont vous l'accusez.
15 Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa,
Hérode non plus, car je vous ai renvoyés à lui, et, vous le voyez, cet homme n'a rien fait qui mérite la mort.
16 saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi.”
Je le relâcherai donc, après l'avoir fait châtier.»
17 [Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin.]
[Or il était obligé à chaque fête de leur relâcher un prisonnier]
18 Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, “A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!”
Mais ils crièrent tous à la fois: «Fais-le mourir! Relâche-nous Barabbas.»
19 Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
Ce Barabbas avait été mis en prison pour une sédition qui avait eu lieu dans la ville, et pour un meurtre.
20 Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu.
Pilate, qui désirait relâcher Jésus, les harangua donc de nouveau;
21 Amma suka yi ihu, cewa, “A giciye shi, a giciye shi.”
mais ils répondirent par les cris de «crucifie-le! crucifie-le!»
22 Sai ya sake ce masu sau na uku, “Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi.”
Il leur dit pour la troisième fois: «Quel mal a-t-il donc fait? Je n'ai rien trouvé en lui qui mérite la mort; je le relâcherai donc, après l'avoir fait châtier?»
23 Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus.
Mais ils insistèrent, demandant à grands cris qu'il fût crucifié, et leurs clameurs et celles des principaux sacrificateurs prévalurent,
24 Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so.
et Pilate prononça que ce qu'ils demandaient serait exécuté:
25 Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.
il leur relâcha celui qui avait été mis en prison pour sédition et pour meurtre, et qu'ils réclamaient; et il leur abandonna Jésus.
26 Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.
Comme ils l'emmenaient au supplice, ils prirent un nommé Simon, de Cyrène, qui venait des champs, et ils le chargèrent de la croix, pour qu'il la portât derrière Jésus.
27 Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa.
Or, Jésus était suivi d'une grande foule de peuple, et particulièrement de femmes qui se frappaient la poitrine et pleuraient sur lui.
28 Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, “Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.
Il se tourna vers elles, et leur dit: «Filles de Jérusalem, ne pleurez pas sur moi, mais pleurez sur vous-mêmes et sur vos enfants;
29 Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.'
car les temps viennent où l’on dira: «Heureuses les stériles! Heureux le sein qui n'a point enfanté! Heureuses les mamelles qui n'ont point nourri!»
30 Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.'
Alors on se mettra à dire aux montagnes: «Tombez sur nous; » et aux collines: «Couvrez-nous; »
31 Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?”
car si l'on fait ces choses au bois vert, que fera-t-on au bois sec?»
32 Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.
Les soldats conduisaient en même temps deux malfaiteurs pour être mis à mort avec lui.
33 Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu.
Quand ils furent arrivés au lieu appelé Calvaire, ils y crucifièrent Jésus, ainsi que les malfaiteurs, l'un à sa droite, l'autre à sa gauche;
34 Yesu yace, “Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba.” Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.
et Jésus dit: «Père, pardonne-leur, car ils ne savent ce qu'ils font.» Ils se partagèrent ses vêtements en les tirant au sort.
35 Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, “Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan.”
Le peuple était là qui regardait. Les sénateurs se moquaient et disaient: «Il en a sauvé d'autres, qu'il se sauve lui-même, s'il est le Messie, l'élu de Dieu.»
36 Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami,
Les soldats aussi, s'approchant pour lui présenter du vinaigre, le raillaient,
37 suna cewa, “Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka.”
et disaient: «Si tu es le roi des Juifs, sauve-toi toi-même.»
38 Akwai wata alama bisansa, “Wannan shine Sarkin Yahudawa.”
Il y avait même une inscription au-dessus de sa tête, portant: «Celui-ci est le Roi des Juifs.»
39 Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, “Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu.”
L'un des malfaiteurs pendus à la croix, l'injuriait, disant: «N'es-tu pas le Messie? Sauve-toi toi-même, et nous avec toi.»
40 Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, “Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa?
Mais l'autre le reprenait: «N'as-tu point de crainte de Dieu, toi qui subis le même jugement?
41 Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba.”
Pour nous, c'est justice; car nous recevons la peine que nos crimes ont méritée; mais lui, il n'a rien fait de mal.»
42 Sai ya kara, “Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka.”
Et il dit à Jésus: «Souviens-toi de moi, quand tu seras dans ton règne.»
43 Yesu ya ce masa, “Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi.”
Et Jésus répondit: «Je te dis en vérité, qu'aujourd'hui même tu seras avec moi dans le paradis.»
44 Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara
Il était déjà environ la sixième heure, quand des ténèbres se répandirent sur tout le pays jusqu’à la neuvième heure.
45 sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.
Le soleil pâlit; le voile du temple se déchira par le milieu;
46 Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, “Uba, na mika Ruhu na a hannunka.” Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu.
et Jésus s'écria d'une voix forte: «Père, je remets mon esprit entre tes mains.» En prononçant ces mots, il expira.
47 Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, “Lallai wannan mutumin mai adalci ne.”
Le centurion, témoin de ces événements, donna gloire à Dieu, disant: «Assurément cet homme était juste; »
48 Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu.
et les foules que ce spectacle avait attirées, voyant ce qui s'était passé, s'en retournaient toutes en se frappant la poitrine.
49 Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.
Mais tous ceux qui connaissaient Jésus, et les femmes qui l'avaient suivi de Galilée, se tenaient là, à l'écart, regardant ce qui se passait.
50 Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne
Il y avait un sénateur, nommé Joseph, homme droit et juste,
51 (bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.
qui ne s'était associé ni au dessein, ni aux actes des autres sénateurs; il était originaire d'Arimathée. ville des Juifs, et il attendait le royaume de Dieu.
52 Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu.
Il se rendit auprès de Pilate et lui demanda le corps de Jésus.
53 Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.
Il le descendit de la croix, l'enveloppa d'un linceul, et le déposa dans un sépulcre taillé dans le roc, où personne n'avait encore été mis.
54 Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato.
C'était le jour de la préparation, et le sabbat allait commencer.
55 Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi.
Les femmes qui étaient venues de la Galilée avec Jésus, ayant accompagné Joseph, virent le sépulcre et la manière dont le corps de Jésus y fut placé,
56 Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.
puis, s'en étant retournées, elles préparèrent des aromates et des parfums.

< Luka 23 >