< Luka 23 >

1 Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus.
And having risen up all the multitude of them (they led *N+kO) Him to Pilate.
2 Suka fara saransa, cewa “Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki.”
They began then to accuse Him saying; This [man] we found misleading the nation (of us *NO) and forbidding tribute to Caesar to be given (and *no) declaring Himself Christ a king to be.
3 Bilatus ya tambaye shi, cewa “Shin kaine Sarkin Yahudawa?” Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Haka ka ce.”
And Pilate (asked *N+kO) Him saying; You yourself are the King of the Jews? And answering him He was saying; You yourself say.
4 Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, “Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba.”
And Pilate said to the chief priests and the crowds; No [thing] find I guilty in man this.
5 Amma suka yi ta cewa, “Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri.”
But they were insisting saying that He stirs up the people teaching throughout all of Judea (and *no) He has begun from Galilee until here.
6 Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline.
Pilate now having heard (Galilee *KO) asked whether the man a Galilean is,
7 Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
and having learned that from the jurisdiction of Herod He is, he sent up Him to Herod being also he himself in Jerusalem in those days.
8 Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi.
And Herod having seen Jesus [was] glad exceedingly; he was for of (long *N+kO) time wishing to see Him because of hearing (many things *K) concerning Him and he was hoping some sign to see by Him done.
9 Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba.
He was questioning then Him in words many; He himself however no [thing] answered him.
10 Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
Had been standing by now the chief priests and the scribes vehemently accusing Him.
11 Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus.
Having set at naught then Him (also *no) Herod with the troops of him and having mocked [and] having put on (Him *ko) apparel splendid, sent back Him to Pilate.
12 Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).
Became then friends both Herod and Pilate on that day with one another; they were formerly for at enmity they were between (them. *N+k+o)
13 Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar,
Pilate then having called together the chief priests and the rulers and the people
14 sai ya ce masu, “Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
said to them; You brought to me man this as misleading the people; and behold I myself before you having examined [Him] no [thing] found in man this guilty of that accusation you are bringing against Him;
15 Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa,
But not even [did] Herod; (he sent back *N+KO) for Him to (us *N+KO) And behold no [thing] worthy of death is done by Him.
16 saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi.”
Having chastised therefore Him I will release [Him].
17 [Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin.]
(necessity *KO) (now had to release to them according to feast one. *K)
18 Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, “A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!”
(They cried out *N+kO) however all together saying; do remove this [man], do release now to us Barabbas;
19 Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
who was on account of insurrection a certain having been made in the city and murder (being cast into *N+kO) (the *no) (prison. *N+kO)
20 Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu.
Again (therefore *N+kO) Pilate called to them wishing to release Jesus.
21 Amma suka yi ihu, cewa, “A giciye shi, a giciye shi.”
But they were crying out saying; (do crucify do crucify *N+kO) Him.
22 Sai ya sake ce masu sau na uku, “Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi.”
And a third [time] he said to them; What for evil did commit this [man]? No [thing] worthy of death found I in Him. Having chastised therefore Him I will release [Him].
23 Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus.
But they were urgent with voices loud asking for Him to be crucified, And were prevailing the voices of them (and of the chief priests. *KO)
24 Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so.
(and *N+kO) Pilate sentenced to be done the demand of them.
25 Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.
He released then (to them *k) the [one] on account of insurrection and murder cast into prison whom they were asking for; and Jesus he delivered to the will of them.
26 Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.
And as they led away Him, having laid hold on (Simon a certain from Cyrene *N+kO) (who *k) (is coming *N+kO) from [the] country they put upon him the cross to carry behind Jesus.
27 Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa.
Were following now Him a great multitude of the people and of women who (also *k) were mourning and they were lamenting for Him.
28 Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, “Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.
Having turned then to them Jesus said; Daughters of Jerusalem, not do weep for Me myself, but for yourselves do weep and for the children of you.
29 Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.'
For behold are coming days in which they will say; Blessed [are] the barren and (the *no) wombs that never did bear and breasts that never (they feed. *N+kO)
30 Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.'
Then They will begin to say to the mountains; do fall upon us; and to the hills; do cover us.
31 Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?”
For if in the green tree these things they do, in the dry what may happen?
32 Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.
Were being led away now also other criminals two with Him to be executed.
33 Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu.
And when (they came *N+kO) to the place which is being called [The] Skull, there they crucified Him and the criminals, the one on [the] right, another and on [the] left.
34 Yesu yace, “Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba.” Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.
And Jesus was saying; Father, do forgive them; not for they know what they do. Dividing then the garments of Him they cast (lots. *NK+o)
35 Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, “Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan.”
And had stood the people beholding. Were deriding [Him] then also the rulers (with them *k) saying; Others He saved, he should save Himself if this is the Christ of God (the *no) Chosen [One].
36 Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami,
(Mocked *N+kO) then Him also the soldiers coming near, (and *k) sour wine offering to Him
37 suna cewa, “Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka.”
and saying; If You yourself are the King of the Jews, do save Yourself!
38 Akwai wata alama bisansa, “Wannan shine Sarkin Yahudawa.”
There was now also an inscription (written *K+o) over Him (writings in Greek and in Latin and in Hebrew; is *K) the King of the Jews This [is].
39 Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, “Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu.”
One now of those having been hanged criminals he was denigrating Him saying: (Surely *N+KO) you yourself are the Christ? do save Yourself and us!
40 Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, “Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa?
Answering now the other (rebuking *N+kO) him (was speaking; *N+kO) Not even do fear you yourself God that under the same judgment you are?
41 Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba.”
and we ourselves indeed justly, Worthy for of what we did we are receiving; [this] man however no [thing] wrong did.
42 Sai ya kara, “Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka.”
And he was saying: Jesus, do remember me (Lord *K) when You may come (into *N+kO) (the kingdom *NK+o) of You!
43 Yesu ya ce masa, “Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi.”
And He said to him (Jesus: *ko) Amen to you I say: today with Me you will be in Paradise.
44 Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara
(And *no) it was (now *k) (already *no) about [the] hour sixth, and darkness came over all the land until [the] hour ninth
45 sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.
(and *ko) (The sun darkened. *N+kO) (and *ko) was torn (then *no) the veil of the temple in [the] middle.
46 Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, “Uba, na mika Ruhu na a hannunka.” Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu.
And having called out in a voice loud Jesus said; Father, into [the] hands of You (I myself commit *N+kO) the Spirit of Mine. (This now *N+kO) having said He breathed His last.
47 Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, “Lallai wannan mutumin mai adalci ne.”
Having seen now the centurion that having taken place (he was glorifying *N+kO) God saying; Certainly man this righteous was.
48 Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu.
And all the having come together crowds to spectacle this, (having seen *N+kO) the [things] having taken place, beating (their own *k) breasts were returning [home].
49 Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.
Had stood now all those who knew (with Him *N+kO) (from *no) afar off also women those (having followed *N+kO) Him from Galilee beholding these things.
50 Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne
And behold a man named Joseph a Council member being (also *n) a man good and righteous;
51 (bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.
he not was having consented to the counsel and to the deed of them; from Arimathea a city of the Jews, who (and *k) he was waiting for (and himself *k) the kingdom of God,
52 Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu.
He having gone to Pilate asked [for] the body of Jesus.
53 Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.
And having taken down (it *k) he wrapped it in a linen cloth and placed (it *N+kO) in a tomb cut in a rock in which no were no [one] (not yet *N+kO) laid.
54 Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato.
And [the] Day it was (of Preparation, *NK+o) and Sabbath was just beginning.
55 Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi.
Having followed then (and *k) (the *no) women who were having come from Galilee with Him saw the tomb and how was laid the body of Him.
56 Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.
Having returned then they prepared spices and anointing oils And on the indeed Sabbath they rested according to the commandment.

< Luka 23 >