< Luka 22 >

1 Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
Now the feast of unleavened bread drew nigh, which is called the Passover.
2 Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
And the chief priests and the scribes sought how they might put him to death; for they feared the people.
3 Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
And Satan entered into Judas who was called Iscariot, being of the number of the twelve.
4 Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
And he went away, and communed with the chief priests and captains, how he might deliver him unto them.
5 Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
And they were glad, and covenanted to give him money.
6 Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
And he consented, and sought opportunity to deliver him unto them in the absence of the multitude.
7 Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
And the day of unleavened bread came, on which the passover must be sacrificed.
8 Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
And he sent Peter and John, saying, Go and make ready for us the passover, that we may eat.
9 Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
And they said unto him, Where wilt thou that we make ready?
10 Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
And he said unto them, Behold, when ye are entered into the city, there shall meet you a man bearing a pitcher of water; follow him into the house whereinto he goeth.
11 Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
And ye shall say unto the goodman of the house, The Master saith unto thee, Where is the guest-chamber, where I shall eat the passover with my disciples?
12 Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
And he will shew you a large upper room furnished: there make ready.
13 Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
And they went, and found as he had said unto them: and they made ready the passover.
14 Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
And when the hour was come, he sat down, and the apostles with him.
15 Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
And he said unto them, With desire I have desired to eat this passover with you before I suffer:
16 Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
for I say unto you, I will not eat it, until it be fulfilled in the kingdom of God.
17 Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
And he received a cup, and when he had given thanks, he said, Take this, and divide it among yourselves:
18 Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
for I say unto you, I will not drink from henceforth of the fruit of the vine, until the kingdom of God shall come.
19 Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
And he took bread, and when he had given thanks, he brake it, and gave to them, saying, This is my body which is given for you: this do in remembrance of me.
20 Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
And the cup in like manner after supper, saying, This cup is the new covenant in my blood, [even] that which is poured out for you.
21 Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
But behold, the hand of him that betrayeth me is with me on the table.
22 Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
For the Son of man indeed goeth, as it hath been determined: but woe unto that man through whom he is betrayed!
23 Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
And they began to question among themselves, which of them it was that should do this thing.
24 Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
And there arose also a contention among them, which of them is accounted to be greatest.
25 Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
And he said unto them, The kings of the Gentiles have lordship over them; and they that have authority over them are called Benefactors.
26 Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
But ye [shall] not [be] so: but he that is the greater among you, let him become as the younger; and he that is chief, as he that doth serve.
27 Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
For whether is greater, he that sitteth at meat, or he that serveth? is not he that sitteth at meat? but I am in the midst of you as he that serveth.
28 Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
But ye are they which have continued with me in my temptations;
29 Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
and I appoint unto you a kingdom, even as my Father appointed unto me,
30 domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
that ye may eat and drink at my table in my kingdom; and ye shall sit on thrones judging the twelve tribes of Israel.
31 Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
Simon, Simon, behold, Satan asked to have you, that he might sift you as wheat:
32 Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
but I made supplication for thee, that thy faith fail not: and do thou, when once thou hast turned again, stablish thy brethren.
33 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
And he said unto him, Lord, with thee I am ready to go both to prison and to death.
34 Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
And he said, I tell thee, Peter, the cock shall not crow this day, until thou shalt thrice deny that thou knowest me.
35 Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
And he said unto them, When I sent you forth without purse, and wallet, and shoes, lacked ye any thing? And they said, Nothing.
36 Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
And he said unto them, But now, he that hath a purse, let him take it, and likewise a wallet: and he that hath none, let him sell his cloke, and buy a sword.
37 Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
For I say unto you, that this which is written must be fulfilled in me, And he was reckoned with transgressors: for that which concerneth me hath fulfillment.
38 Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
And they said, Lord, behold, here are two swords. And he said unto them, It is enough.
39 Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
And he came out, and went, as his custom was, unto the mount of Olives; and the disciples also followed him.
40 Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
And when he was at the place, he said unto them, Pray that ye enter not into temptation.
41 Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
And he was parted from them about a stone’s cast; and he kneeled down and prayed,
42 yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
saying, Father, if thou be willing, remove this cup from me: nevertheless not my will, but thine, be done.
43 Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
And there appeared unto him an angel from heaven, strengthening him.
44 Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
And being in an agony he prayed more earnestly: and his sweat became as it were great drops of blood falling down upon the ground.
45 Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
And when he rose up from his prayer, he came unto the disciples, and found them sleeping for sorrow,
46 sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
and said unto them, Why sleep ye? rise and pray, that ye enter not into temptation.
47 Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
While he yet spake, behold, a multitude, and he that was called Judas, one of the twelve, went before them; and he drew near unto Jesus to kiss him.
48 amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
But Jesus said unto him, Judas, betrayest thou the Son of man with a kiss?
49 Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
And when they that were about him saw what would follow, they said, Lord, shall we smite with the sword?
50 Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
And a certain one of them smote the servant of the high priest, and struck off his right ear.
51 Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
But Jesus answered and said, Suffer ye thus far. And he touched his ear, and healed him.
52 Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
And Jesus said unto the chief priests, and captains of the temple, and elders, which were come against him, Are ye come out, as against a robber, with swords and staves?
53 Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
When I was daily with you in the temple, ye stretched not forth your hands against me: but this is your hour, and the power of darkness.
54 Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
And they seized him, and led him [away], and brought him into the high priest’s house. But Peter followed afar off.
55 Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
And when they had kindled a fire in the midst of the court, and had sat down together, Peter sat in the midst of them.
56 Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
And a certain maid seeing him as he sat in the light [of the fire], and looking stedfastly upon him, said, This man also was with him.
57 Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
But he denied, saying, Woman, I know him not.
58 Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
And after a little while another saw him, and said, Thou also art [one] of them. But Peter said, Man, I am not.
59 Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
And after the space of about one hour another confidently affirmed, saying, Of a truth this man also was with him: for he is a Galilaean.
60 Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
But Peter said, Man, I know not what thou sayest. And immediately, while he yet spake, the cock crew.
61 Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
And the Lord turned, and looked upon Peter. And Peter remembered the word of the Lord, how that he said unto him, Before the cock crow this day, thou shalt deny me thrice.
62 Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
And he went out, and wept bitterly.
63 Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
And the men that held [Jesus] mocked him, and beat him.
64 Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
And they blindfolded him, and asked him, saying, Prophesy: who is he that struck thee?
65 Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
And many other things spake they against him, reviling him.
66 Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
And as soon as it was day, the assembly of the elders of the people was gathered together, both chief priests and scribes; and they led him away into their council, saying,
67 suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
If thou art the Christ, tell us. But he said unto them, If I tell you, ye will not believe:
68 idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
and if I ask [you], ye will not answer.
69 Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
But from henceforth shall the Son of man be seated at the right hand of the power of God.
70 Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
And they all said, Art thou then the Son of God? And he said unto them, Ye say that I am.
71 Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”
And they said, What further need have we of witness? for we ourselves have heard from his own mouth.

< Luka 22 >