< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Взглянув же, Он увидел богатых, клавших дары свои в сокровищницу;
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
увидел также и бедную вдову, положившую туда две лепты,
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
и сказал: истинно говорю вам, что эта бедная вдова больше всех положила;
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
ибо все те от избытка своего положили в дар Богу, а она от скудости своей положила все пропитание свое, какое имела.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
И когда некоторые говорили о храме, что он украшен дорогими камнями и вкладами, Он сказал:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
придут дни, в которые из того, что вы здесь видите, не останется камня на камне; все будет разрушено.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
И спросили Его: Учитель! когда же это будет? и какой признак, когда это должно произойти?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Он сказал: берегитесь, чтобы вас не ввели в заблуждение, ибо многие придут под именем Моим, говоря, что это Я; и это время близко: не ходите вслед их.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Когда же услышите о войнах и смятениях, не ужасайтесь, ибо этому надлежит быть прежде; но не тотчас конец.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Тогда сказал им: восстанет народ на народ, и царство на царство;
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
будут большие землетрясения по местам, и глады, и моры, и ужасные явления, и великие знамения с неба.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Прежде же всего того возложат на вас руки и будут гнать вас, предавая в синагоги и в темницы, и поведут пред царей и правителей за имя Мое;
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
будет же это вам для свидетельства.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Итак положите себе на сердце не обдумывать заранее, что отвечать,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
ибо Я дам вам уста и премудрость, которой не возмогут противоречить ни противостоять все, противящиеся вам.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Преданы также будете и родителями, и братьями, и родственниками, и друзьями, и некоторых из вас умертвят;
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
и будете ненавидимы всеми за имя Мое,
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
но и волос с головы вашей не пропадет, -
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
терпением вашим спасайте души ваши.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Когда же увидите Иерусалим, окруженный войсками, тогда знайте, что приблизилось запустение его:
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
тогда находящиеся в Иудее да бегут в горы; и кто в городе, выходи из него; и кто в окрестностях, не входи в него,
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
потому что это дни отмщения, да исполнится все написанное.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Горе же беременным и питающим сосцами в те дни; ибо великое будет бедствие на земле и гнев на народ сей:
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
и падут от острия меча, и отведутся в плен во все народы; и Иерусалим будет попираем язычниками, доколе не окончатся времена язычников.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
И будут знамения в солнце и луне и звездах, а на земле уныние народов и недоумение; и море восшумит и возмутится;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
люди будут издыхать от страха и ожидания бедствий, грядущих на вселенную, ибо силы небесные поколеблются,
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
и тогда увидят Сына Человеческого, грядущего на облаке с силою и славою великою.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Когда же начнет это сбываться, тогда восклонитесь и поднимите головы ваши, потому что приближается избавление ваше.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
И сказал им притчу: посмотрите на смоковницу и на все деревья:
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
когда они уже распускаются, то, видя это, знаете сами, что уже близко лето.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Так, и когда вы увидите то сбывающимся, знайте, что близко Царствие Божие.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Истинно говорю вам: не прейдет род сей, как все это будет;
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
небо и земля прейдут, но слова Мои не прейдут.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Смотрите же за собою, чтобы сердца ваши не отягчались объедением и пьянством и заботами житейскими, и чтобы день тот не постиг вас внезапно,
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
ибо он, как сеть, найдет на всех живущих по всему лицу земному;
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
итак бодрствуйте на всякое время и молитесь, да сподобитесь избежать всех сих будущих бедствий и предстать пред Сына Человеческого.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Днем Он учил в храме, а ночи, выходя, проводил на горе, называемой Елеонскою.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
И весь народ с утра приходил к Нему в храм слушать Его.

< Luka 21 >