< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Ele olhou para cima e viu as pessoas ricas que estavam colocando seus presentes na tesouraria.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Ele viu uma certa viúva pobre fundida em duas pequenas moedas de latão.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Ele disse: “Em verdade vos digo, esta pobre viúva colocou mais do que todas elas,
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
por todas estas colocadas em presentes para Deus a partir de sua abundância, mas ela, fora de sua pobreza, colocou em tudo o que tinha para viver”.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Enquanto alguns falavam sobre o templo e como foi decorado com belas pedras e presentes, ele disse:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
“Quanto a estas coisas que você vê, virão os dias em que não ficará aqui uma pedra sobre outra que não será jogada para baixo”.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Eles lhe perguntaram: “Professor, então quando serão essas coisas? Qual é o sinal de que estas coisas estão prestes a acontecer”?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Ele disse: “Cuidado para não se perderem, pois muitos virão em meu nome, dizendo: 'Eu sou ele', e: 'O tempo está próximo'. Portanto, não os siga.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Quando ouvir falar de guerras e distúrbios, não se assuste, pois estas coisas devem acontecer primeiro, mas o fim não virá imediatamente”.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Então ele lhes disse: “Nação se levantará contra nação, e reino contra reino”.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
Haverá grandes terremotos, fomes e pragas em vários lugares. Haverá terremotos e grandes sinais do céu.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Mas antes de todas estas coisas, eles colocarão suas mãos sobre você e o perseguirão, entregando-o a sinagogas e prisões, trazendo-o diante de reis e governadores por causa do meu nome.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Será um testemunho para vocês.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Portanto, não mediteis de antemão em vossos corações como responder,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
pois eu vos darei uma boca e uma sabedoria que todos os vossos adversários não poderão suportar ou contradizer.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Você será entregue até mesmo por pais, irmãos, parentes e amigos. Eles farão com que alguns de vocês sejam condenados à morte.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Vocês serão odiados por todos os homens por causa do meu nome.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
E nem um fio de cabelo de sua cabeça perecerá.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
“Com sua resistência, vocês ganharão suas vidas.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
“Mas quando você vir Jerusalém cercada por exércitos, então saiba que sua desolação está próxima.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Então, deixe que aqueles que estão na Judéia fujam para as montanhas. Deixem partir aqueles que estão no meio dela. Que aqueles que estão no país não entrem nele.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Pois estes são dias de vingança, para que todas as coisas que estão escritas possam ser cumpridas.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Ai daqueles que estão grávidos e daqueles que amamentam bebês naqueles dias! Pois haverá grande angústia na terra e ira para este povo.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Eles cairão pelo fio da espada, e serão levados cativos a todas as nações. Jerusalém será pisoteada pelos gentios até que os tempos dos gentios sejam cumpridos.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
“Haverá sinais no sol, na lua e nas estrelas; e na terra ansiedade das nações, em perplexidade pelo rugido do mar e das ondas;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
homens desmaiando por medo e por expectativa das coisas que estão vindo sobre o mundo, pois os poderes dos céus serão abalados.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Então eles verão o Filho do Homem vindo em uma nuvem com poder e grande glória.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Mas quando estas coisas começarem a acontecer, olhem para cima e levantem suas cabeças, porque sua redenção está próxima”.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Ele lhes contou uma parábola. “Veja a figueira e todas as árvores”.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Quando elas já estão brotando, você vê e sabe por si mesmo que o verão já está próximo.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Mesmo assim, vocês também, quando virem estas coisas acontecendo, saibam que o Reino de Deus está próximo.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Certamente eu lhes digo que esta geração não passará até que todas as coisas estejam concluídas.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
O céu e a terra passarão, mas minhas palavras não passarão de forma alguma.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
“Portanto, tenham cuidado, ou seus corações ficarão carregados de carinho, embriaguez e preocupações com esta vida, e esse dia chegará repentinamente”.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
Pois ele virá como um laço sobre todos aqueles que habitam na superfície de toda a terra.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Portanto, estejam sempre vigilantes, orando para que sejam considerados dignos de escapar de todas essas coisas que acontecerão, e de se apresentarem diante do Filho do Homem”.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Every dia Jesus estava ensinando no templo, e todas as noites ele saía e passava a noite na montanha que se chama Olivet.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Todas as pessoas vinham de manhã cedo até ele no templo para ouvi-lo.

< Luka 21 >