< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Og da han så op, fikk han se de rike legge sine gaver i tempelkisten.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Og han så en fattig enke legge to skjerver i den.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Da sa han: Sannelig sier jeg eder: Denne fattige enke har lagt mere enn alle.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
For alle disse la sine gaver av sin overflod; men hun la av sin fattigdom alt det hun hadde å leve av.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Og da nogen sa om templet at det var prydet med fagre stener og tempelgaver, sa han:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
Dette som I ser - de dager skal komme da det ikke skal levnes sten på sten som ikke skal brytes ned.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Da spurte de ham og sa: Mester! når skal da dette skje? og hvad skal tegnet være når dette skal skje?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Og han sa: Se til at I ikke føres vill! for mange skal komme i mitt navn og si: Det er mig, og: Tiden er nær. Gå ikke efter dem!
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Og når I får høre om krig og oprør, da la eder ikke skremme! for dette må først skje, men enden kommer ikke med det samme.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Da sa han til dem: Folk skal reise sig mot folk og rike mot rike,
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
og store jordskjelv skal det være og hunger og sott både her og der, og det skal skje forferdelige ting og store tegn fra himmelen.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Men før alt dette skjer, skal de legge hånd på eder og forfølge eder og overgi eder til synagoger og fengsler, og I skal føres frem for konger og landshøvdinger for mitt navns skyld;
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
det skal falle ut til godt vidnesbyrd for eder.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Legg eder derfor på hjerte at I ikke forut skal grunde på hvorledes I skal forsvare eder!
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
for jeg skal gi eder munn og visdom som alle eders motstandere ikke kan motstå eller motsi.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Men I skal forrådes endog av foreldre og brødre og frender og venner, og de skal volde nogen av eder døden,
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
og I skal hates av alle for mitt navns skyld.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Og ikke et hår på eders hode skal gå tapt.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
Vær tålmodige, så skal I vinne eders sjeler!
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Men når I ser Jerusalem bli kringsatt av krigshærer, da skal I vite at dets ødeleggelse er nær.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Da må de som er i Judea, fly til fjells, og de som er inne i byen, må gå ut, og de som er ute på landet, ikke gå inn i den;
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
for dette er gjengjeldelsens dager, forat alt det som skrevet er, skal bli opfylt.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Men ve de fruktsommelige, og dem som gir die, i de dager! for stor nød skal være på jorden, og vrede over dette folk,
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
og de skal falle for sverds egg og føres fangne til alle folkeslag, og Jerusalem skal ligge nedtrådt av hedninger, inntil hedningenes tid er til ende.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Og det skal skje tegn i sol og måne og stjerner, og på jorden skal folkene engstes i fortvilelse når hav og brenninger bruser,
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
mens mennesker faller i avmakt av redsel og gru for det som kommer over jorderike; for himmelens krefter skal rokkes.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Og da skal de se Menneskesønnen komme i skyen med kraft og megen herlighet.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Men når dette begynner å skje, da rett eder op og løft eders hoder! for eders forløsning stunder til.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Og han sa en lignelse til dem: Se på fikentreet og alle trær:
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Så snart de springer ut og I ser det, da vet I av eder selv at nu er sommeren nær.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Således skal også I, når I ser dette skje, vite at Guds rike er nær.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Sannelig sier jeg eder: Denne slekt skal ingenlunde forgå før det skjer alt sammen.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Himmel og jord skal forgå, men mine ord skal ingenlunde forgå.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Men vokt eder at ikke eders hjerte nogen tid tynges av rus og svir og timelige bekymringer, så hin dag kommer uventet over eder som en snare!
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
for den skal komme over alle dem som bor over den hele jord.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Men våk hver tid og stund, og bed, så I kan være i stand til å undfly alt dette som skal komme, og til å bli stående for Menneskesønnen!
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Om dagene lærte han i templet, men om nettene gikk han ut av byen og overnattet på det berg som kalles Oljeberget.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Og alt folket kom tidlig om morgenen til ham i templet for å høre ham.

< Luka 21 >