< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Aa ie niandra, nahavazoho mpañaleale nampigodrom-bola amy fanontonan-dralay;
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
nioni’e ka ty vantotse rarake nampijoñe drala roe.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Le hoe re: Eka! to t’itaroñako te bey ty nengae’ ty vantotse misotry tia te am’ iabikey;
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
fa ami’ty habeim-panaña’ iareo ty nampijoña’ iareo am-panontonam-baran’ Añahare ao; fe ami’ty harotà’e ty nampibiroña’e ty sehangam-piveloma’e.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Teo te nivesovesoe’ ty ila’e i Anjom­ban’ Añaharey, t’ie nihamineñe vato soa naho ravoravo; le hoe re:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
Ty amo raha isa’ areoo, mbe ho tondroke ty andro tsy hampidonañe vato raike ambone’ ty ila’e ze tsy haretsak’ ambane.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Le nañontanea’ iareo ty hoe: O Talè, mbia t’ie ho tendreke? Le inoñe ty ho viloñe hiaolo ty hifetsaha’e?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Le hoe re: Asoao tsy hampandridriheñe. Fa maro ty ho pok’eo hieva ty añarako, hanao ty hoe: Izaho ty ie, naho ty hoe: Fa antitotse i àndroy. Ko oriheñe.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Ie mitsanoñ’ aly ndra fivalitaboahañe, ko vorombelo; fa tsi-mete tsy ho avy hey izay, fe mbe tsy aniany i hamodoañey.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Le hoe re am’iereo: Fifelehañe ty hitroatse hiatre-pifelehañe naho fifeheañe ty hiatre-pifeheañe.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
Ho an-koe an-koe ty ezeñezen-tane jabajaba naho san-kasalikoañe vaho hiboake eo ty raha mampirevendreveñe naho ty viloñe ra’elahy hirik’ andindìñe añe.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Fe aolo’ irezay, ho tsepahem-pità’ iareo nahareo, hanoeñe sampore­rake naho hasese am-pitontonañe naho ambalabey ao vaho hampiatrefeñe mpanjaka naho roandriañe ty ami’ty añarako.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
F’ie hivalike ho fitaroña’ areo.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Aa le ampifahàro añ’ arofo’areo te tsy hisafiry miaolo ze hatoi’ areo,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
amy te homeiko falie naho hihitse tsy ho lefe’ ty rafelahi’ areo toiñeñe ndra rebaheñe.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Le hifotetse ama’ areo o raeo naho o rahalahio naho o longoo vaho o rañetseo le havetrake ty ila’areo.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Ho heje’ ze kila ondaty nahareo ty ami’ty añarako.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Fe tsy ho po-maròy raike o añambone’areoo.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
Ty fahaliñisa’areo ro fandrombaham-piaiñe.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Aa naho isa’ areo te arikoboñen-dahin-defoñe t’Ierosaleme; le maharendreha te an-titotse ty hampangoakoaheñ’ aze
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Ee te hivo­ratsake mb’am-bohitse eñe o e Iehodào, naho hitriban-day ze e Ierosaleme ao vaho tsy hizilik’ ao o am-pariparits’ añeo.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Izay o andro fandilovañeo hañenefañe ze hene pinatetse.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Hekoheko ho ami’ty mivesatse naho ty mampinono amy andro rezay! Fa haoream-bey ty hizò amy Taney vaho haviñerañe am’ondaty retoa,
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
ie hatsingoron-delam-pibara naho ho tantalieñe am-bozo-tali-am-baniañe mb’ amy ze kila tane añe vaho ho lialià’ o kilakila ‘ndatio t’Ierosaleme ampara’ te heneke ty sa’ o kilakila ondatio.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Le hiboak’ amy androy naho amy volañey naho amo vasiañeo ty viloñe vaho halovilovy am-pioremèñañe o fifeheañeo ty amy fitroña’ i riakey naho ty fivalitaboaha’e;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
ho tsipike ty anifañe ondatio ami’ty faha­oniña’e o hifetsak’ an-tane atoio; le hampihendrahendraeñe o haozaran-dikerañeo.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Ho oni’ iereo mitotsake mb’eo amy zao amo rahoñeo eñe an-kaozarañe naho engeñe ra’elahy i Ana’ondatiy.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Ie mamototse hiboake, le mijohaña naho miandradrà, fa an-titotse ty fijebañañe anahareo.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Le hoe ty nandrazaña’e: Hehe o sakoañeo naho ze hene hatae.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Ie mibotiboty le inao te an-titotse ty lohataoñe.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Hoe izay ka te isa’areo ty fifetsaha’ o tsa­raeñeo le fohino te mitotoke i Fifehean’ Añaharey.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Eka! to t’itaroñako te tsy ho kapioke ty tariratse toy naho tsy heneke hey irezay.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Himiañe añe o likerañeo naho ty tane toy, fe tsy ho modo o volakoo.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Mitaoa, tsy mone ho lifore’ ty hatea-haneñe naho ty hajìke vaho ty hasosorañe amo haveloñe zao ty arofo, hera hitojeha ama’ areo i andro zay,
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
toe hanahake fandri-bò ty hivovoa’e amy ze hene mpimoneñe an-tane atoy amy andro zay.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Aa le mitaòa naho mihalalia nainai’e t’ie hañeva handrife amo fonga hifetsakeo vaho hijohañe añatrefa’ i Ana’ondatiy.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Nañoke an-kiririsan’Anjomban’ Añahare eo re boak’andro; f’ie haleñe, nienga mb’eo niam­besatse am-bohi’ Oliva ey.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Naho mbe nangararak’ atiñanañe le nitontoñe hijanjiñe aze añ’ Anjom­ban’ Añahare ao i lahialeñey.

< Luka 21 >