< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
respiciens autem vidit eos qui mittebant munera sua in gazofilacium divites
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
vidit autem et quandam viduam pauperculam mittentem aera minuta duo
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
et dixit vere dico vobis quia vidua haec pauper plus quam omnes misit
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
nam omnes hii ex abundanti sibi miserunt in munera Dei haec autem ex eo quod deest illi omnem victum suum quem habuit misit
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
et quibusdam dicentibus de templo quod lapidibus bonis et donis ornatum esset dixit
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
haec quae videtis venient dies in quibus non relinquetur lapis super lapidem qui non destruatur
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
interrogaverunt autem illum dicentes praeceptor quando haec erunt et quod signum cum fieri incipient
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
qui dixit videte ne seducamini multi enim venient in nomine meo dicentes quia ego sum et tempus adpropinquavit nolite ergo ire post illos
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
cum autem audieritis proelia et seditiones nolite terreri oportet primum haec fieri sed non statim finis
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
tunc dicebat illis surget gens contra gentem et regnum adversus regnum
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
terraemotus magni erunt per loca et pestilentiae et fames terroresque de caelo et signa magna erunt
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
sed ante haec omnia inicient vobis manus suas et persequentur tradentes in synagogas et custodias trahentes ad reges et praesides propter nomen meum
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
continget autem vobis in testimonium
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
ponite ergo in cordibus vestris non praemeditari quemadmodum respondeatis
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
ego enim dabo vobis os et sapientiam cui non poterunt resistere et contradicere omnes adversarii vestri
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
trademini autem a parentibus et fratribus et cognatis et amicis et morte adficient ex vobis
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
et eritis odio omnibus propter nomen meum
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
et capillus de capite vestro non peribit
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
in patientia vestra possidebitis animas vestras
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
cum autem videritis circumdari ab exercitu Hierusalem tunc scitote quia adpropinquavit desolatio eius
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
tunc qui in Iudaea sunt fugiant in montes et qui in medio eius discedant et qui in regionibus non intrent in eam
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
quia dies ultionis hii sunt ut impleantur omnia quae scripta sunt
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
vae autem praegnatibus et nutrientibus in illis diebus erit enim pressura magna supra terram et ira populo huic
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
et cadent in ore gladii et captivi ducentur in omnes gentes et Hierusalem calcabitur a gentibus donec impleantur tempora nationum
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
et erunt signa in sole et luna et stellis et in terris pressura gentium prae confusione sonitus maris et fluctuum
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
arescentibus hominibus prae timore et expectatione quae supervenient universo orbi nam virtutes caelorum movebuntur
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
et tunc videbunt Filium hominis venientem in nube cum potestate magna et maiestate
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
his autem fieri incipientibus respicite et levate capita vestra quoniam adpropinquat redemptio vestra
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
et dixit illis similitudinem videte ficulneam et omnes arbores
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
cum producunt iam ex se fructum scitis quoniam prope est aestas
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
ita et vos cum videritis haec fieri scitote quoniam prope est regnum Dei
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
amen dico vobis quia non praeteribit generatio haec donec omnia fiant
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
caelum et terra transibunt verba autem mea non transient
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
adtendite autem vobis ne forte graventur corda vestra in crapula et ebrietate et curis huius vitae et superveniat in vos repentina dies illa
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
tamquam laqueus enim superveniet in omnes qui sedent super faciem omnis terrae
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
vigilate itaque omni tempore orantes ut digni habeamini fugere ista omnia quae futura sunt et stare ante Filium hominis
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
erat autem diebus docens in templo noctibus vero exiens morabatur in monte qui vocatur Oliveti
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
et omnis populus manicabat ad eum in templo audire eum

< Luka 21 >