< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Or Jésus, regardant, vit des riches qui mettaient leurs aumônes dans le tronc.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Il vit aussi une pauvre veuve mettant deux petites pièces de monnaie.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Et il dit: En vérité, je vous le dis, cette pauvre veuve a mis plus que tous les autres.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
Car tous ceux-là ont mis pour offrandes à Dieu, de leur superflu; mais elle, elle a mis de son indigence même, tout le vivre qu’elle avait.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Et quelques-uns disant du temple, qu’il était bâti de belles pierres, et orné de dons, il répondit:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
Viendront des jours où de ce que vous voyez, il ne restera pas pierre sur pierre, qui ne soit détruite.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Et ils l’interrogèrent, disant: Maître, quand ces choses arriveront-elles, et quel sera le signe qu’elles commenceront de s’accomplir?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Jésus dit: Prenez garde d’être séduits; car beaucoup viendront en mon nom, disant: C’est moi, et le temps approche; ne les suivez donc point.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Et quand vous entendrez parler de guerres et de séditions, n’en soyez point effrayés; il faut auparavant que ces choses arrivent; mais ce n’est pas encore sitôt la fin.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Alors il leur disait: Une nation se soulèvera contre une nation, un royaume contre un royaume.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
Il y aura de grands tremblements de terre en divers lieux, et des pestes, et des famines, et des signes effrayants dans le ciel, et de grands prodiges.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Mais avant tout cela, on mettra la main sur vous, et on vous persécutera, vous livrant aux synagogues et aux prisons, vous traînant devant les rois et les gouverneurs à cause de mon nom.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Or cela vous arrivera en témoignage.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Mettez donc bien dans vos cœurs de ne point préméditer comment vous répondrez.
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
Car je vous donnerai moi-même une bouche et une sagesse à laquelle tous vos adversaires ne pourront résister, ni rien opposer.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Vous serez livrés par vos pères et vos mères, par vos frères, vos parents et vos amis, et ils en mettront à mort d’entre vous.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Et vous serez en haine à tous à cause de mon nom;
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Mais pas un cheveu de votre tête ne périra.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
C’est par votre patience que vous posséderez vos âmes.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Or, quand vous verrez Jérusalem investie par une armée, sachez que sa désolation est proche:
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Alors, que ceux qui sont dans la Judée fuient vers les montagnes, que ceux qui sont au milieu d’elle s’en éloignent; et que ceux qui sont dans les contrées n’y entrent point.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Parce que ce sont là des jours de vengeance, afin que s’accomplisse tout ce qui est écrit.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Mais malheur aux femmes enceintes et à celles qui nourriront en ces jours-là; car il y aura une détresse affreuse dans le pays, et une grande colère contre ce peuple.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Ils tomberont sous le tranchant du glaive, et seront emmenés captifs dans toutes les nations, et Jérusalem sera foulée aux pieds par les gentils, jusqu’à ce que les temps des nations soient accomplis.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Et il y aura des signes dans le soleil, dans la lune et dans les étoiles; et, sur la terre, la détresse des nations, à cause du bruit confus de la mer et des flots;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
Les hommes séchant de frayeur dans l’attente de ce qui doit arriver à tout l’univers; car les vertus des cieux seront ébranlées;
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Et alors ils verront le Fils de l’homme venant dans une nuée, avec une grande puissance et une grande majesté.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Or, quand ces choses commenceront à s’accomplir, regardez et levez la tête, parce que votre rédemption approche.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Et il leur dit cette comparaison: Voyez le figuier et tous les arbres;
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Quand ils commencent à produire du fruit, vous savez que l’été est proche.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
De même vous, quand vous verrez ces choses arriver, sachez que le royaume de Dieu est proche.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
En vérité, je vous le dis, cette génération ne passera point, jusqu’à ce que toutes ces choses soient accomplies.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Le ciel et la terre passeront; mais mes paroles ne passeront point.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Faites donc attention à vous, de peur que vos cœurs ne s’appesantissent dans la crapule, l’ivresse et les soins de cette vie, et que ce jour ne vienne soudainement sur vous.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
Car, comme un filet, il enveloppera tous ceux qui habitent sur la face de la terre.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Veillez donc et priez en tout temps, afin que vous soyez trouvés dignes d’éviter toutes ces choses qui doivent arriver, et de paraître avec confiance devant le Fils de l’homme.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Or, le jour il enseignait dans le temple; mais la nuit, sortant, il se retirait sur la montagne appelée des Oliviers.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Et tout le peuple venait de grand matin vers lui au temple pour l’écouter.

< Luka 21 >