< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Jésus, levant les yeux, vit les riches qui mettaient leurs offrandes dans le tronc.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Il vit aussi une pauvre veuve qui y mettait deux pites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Et il dit: En vérité, je vous le déclare, cette pauvre veuve a mis plus que tous les autres.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
Car tous ceux-là, pour leurs offrandes, ont donné de leur superflu; mais celle-ci a donné de son indigence, tout ce qu'elle avait pour vivre.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Quelques-uns parlaient du temple, des belles pierres et des dons qui l'ornaient. Jésus dit:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
Les jours viendront où, de ce que vous regardez, il ne restera pas ici une pierre sur une autre pierre qui ne soit renversée.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Alors ils lui demandèrent: Maître, quand donc ces choses arriveront-elles, et à quel signe connaîtra-t-on qu'elles sont sur le point d'arriver?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Il répondit: Prenez garde de ne pas vous laisser séduire; car plusieurs viendront en mon nom, disant: C'est moi qui suis le Christ. Le moment approche! Ne les suivez pas!
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Et quand vous entendrez parler de guerres et de séditions, ne vous effrayez pas, car il faut que ces choses arrivent d'abord; mais ce ne sera pas de sitôt la fin.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Il leur dit aussi: Une nation s'élèvera contre une autre nation, et un royaume contre un autre royaume.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
Il y aura de grands tremblements de terre, des famines et des pestes en divers lieux, des phénomènes effrayants et de grands signes dans le ciel.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Mais avant tout cela, on mettra la main sur vous, on vous persécutera, on vous livrera aux synagogues, on vous mettra en prison; et vous serez traînés devant les rois et devant les gouverneurs, à cause de mon nom.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Cela vous arrivera pour que vous rendiez témoignage.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Mettez-vous donc bien dans l'esprit de ne pas vous préoccuper de votre défense.
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
En effet, je vous donnerai une parole pleine de sagesse, à laquelle tous vos adversaires ne pourront résister ni contredire.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Vous serez livrés même par vos pères et vos mères, par vos frères, vos parents et vos amis; et ils feront mourir plusieurs d'entre vous.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Vous serez haïs de tous, à cause de mon nom.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Mais il ne se perdra pas un cheveu de votre tête.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
C'est par votre patience que vous sauverez vos âmes.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Or, quand vous verrez Jérusalem investie par des armées, sachez, à ce moment-là, que sa ruine approche.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Que ceux qui seront alors dans la Judée s'enfuient dans les montagnes; que ceux qui seront dans l'intérieur de la ville en sortent, et que ceux qui seront dans les champs, ne se retirent pas dans la ville.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Car ce sont là les jours de la vengeance, afin que s'accomplisse tout ce qui est écrit.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Malheur aux femmes qui seront enceintes, et à celles qui allaiteront en ces jours-là! Car il y aura une grande détresse dans le pays et une grande colère contre ce peuple.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Ils tomberont sous le tranchant de l'épée, ils seront emmenés captifs parmi toutes les nations; et Jérusalem sera foulée aux pieds par les Païens, jusqu'à ce que les temps des nations païennes soient accomplis.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Il y aura des signes dans le soleil, dans la lune et dans les étoiles; et, sur la terre, l'angoisse s'emparera des nations troublées par le fracas de la mer et des flots.
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
Les hommes rendront l'âme de frayeur, dans l'attente des maux qui viendront sur le monde; car les puissances des cieux seront ébranlées.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Alors on verra le Fils de l'homme venant sur une nuée, avec une grande puissance et une grande gloire.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Lorsque ces choses commenceront à arriver, redressez-vous et levez vos têtes, parce que votre délivrance est proche.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Puis il leur dit une parabole: Voyez le figuier et tous les autres arbres;
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
quand ils commencent à pousser, vous savez de vous-mêmes, en les voyant, que l'été est déjà proche.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
De même, lorsque vous verrez ces choses arriver, sachez que le royaume de Dieu est proche.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
En vérité, je vous le dis, cette génération ne passera pas, que toutes ces choses n'arrivent.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Le ciel et la terre passeront; mais mes paroles ne passeront point.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Prenez donc garde à vous-mêmes, de peur que vos coeurs ne soient appesantis par les excès de la bonne chère, par l'ivresse et par les inquiétudes, de cette vie, et que ce jour-là ne vienne subitement sur vous,
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
comme un filet; car il surprendra tous ceux qui habitent la surface de la terre entière.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Veillez donc en tout temps et priez, afin que vous puissiez échapper à tous ces maux qui doivent arriver, et subsister devant le Fils de l'homme.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Or, Jésus enseignait dans le temple pendant le jour; mais le soir, il sortait et passait les nuits sur la montagne appelée montagne des Oliviers.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Et, dès le point du jour, tout le peuple venait à lui dans le temple pour l'écouter.

< Luka 21 >